Rigima Na Neman Ɓarkewa a APC, An Dakatar da Tsohon Kakakin Jam'iyyar a Arewa

Rigima Na Neman Ɓarkewa a APC, An Dakatar da Tsohon Kakakin Jam'iyyar a Arewa

  • Jam'iyyar APC ta dakatar da tsohon sakataren yaɗa labarai na jam'iyyar a jihar Kwara, Alhaji Tajuedeen Aro bisa zargin cin amana
  • Shugabannin APC na gundumar Ojumo ta Arewa maso Yamma ne suka sanar da haka a wata wasika da suka tura masa
  • Da yake mayar da martani, Tajuedeen Aro ya zargi shugabannin jam'iyyar da ɗaukae mataki ba tare da bin ƙa'idojin da aka shinfida ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau daɓkullum

Jihar Kwara - Jam'iyyar APC mai mulki ta dakatar da tsohon sakataren yaɗa labaranta, Alhaji Tajuedeen Aro a jihar Kwara.

Shugabannin jam'iyyar na Ojomu ta Arewa maso Yamma sun zargi tsohon kakakin APC da cin amana da zagon ƙasa, shiyasa suka dakatar da shi.

Kara karanta wannan

Arewa na cikin matsala, ambaliya ta ƙara kashe mutum 29, gidaje 321,000 sun lalace

Shugaban APC na kasa, Abdullahi Ganduje.
APC da dakatar da shugaban kakakinta na jihar Kwara, Alhaji Tajuedeen Aro Hoto: Dr. Abdullahi Umar Ganduje
Asali: Twitter

Hakan na kunshe ne a wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 15 ga watan Satumba, 2024 wadda ta shiga hannun jaridar Daily Trust jiya Juma'a.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa APC ta dakatar da jigon?

A cewarsu, sun ɗauki wannan matakin ne domin daƙile yunkurinsa na kawo hargitsi da rabuwar kai a tsakanin ƴaƴan jam'iyyar a matakin gunduma.

A wasiƙar da aka aika wa Alhaji Tajuedeen Aro, shugabannin jam'iyyar suka ce:

"Bisa zarge-zargen da ke kansa na cin amanar jam'iyya, yunƙurin haifar da sabani da rarrabuwar kawuna a cikin jam’iyyar da rashin girmama na gaba, mun yanke hukuncin dakatar da kai ba tare da ɓata lokaci ba."

Tsohon kakakin APC ta maida marani

Da aka tuntuɓe shi, tsohon kakakin APC a jihar Kwara, Alhaji Tajuedeen Aro ya tabbatar da samun wasiƙar dakatar da shi.

Sai dai ya musanta zargin cin amanar jam'iyyar, yana mai zargin shugabannin APC na gundumar da ɗaukar mataki ba tare da bin ƙa'idoji ba.

Kara karanta wannan

Hukumar INEC ta ba zabaɓben gwamnan jihar Edo takarda shaida, bayanai sun fito

Jam'iyyar APC ta lashe zaɓen ciyamomi 16

A wani rahoton kuma hukumar zaben jihar Kwara (KWSIEC) ta sanar da sakamakon zaben kananan hukumomi.

Hukumar ta ce jam'iyyar APC mai mulkin jihar ta yi nasarar lashe duka kujerun kananan hukumomi 16 da aka gudanar ranar Asabar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262