Bayan Shan Mummunan Kaye a Zaben Gwamna, Jam’iyyar LP Ta Ba Peter Obi Laifi

Bayan Shan Mummunan Kaye a Zaben Gwamna, Jam’iyyar LP Ta Ba Peter Obi Laifi

  • Tsagin jam'iyyar LP ta taya dan takarar APC da ya lashe zaben Edo, Monday Okpebholo murnar nasarar zaben jihar
  • Shugaban tsagin jam'iyyar, Julius Abure ya ce faduwar LP a zaben ba ta rasa nasaba da gudunmawar dan takararta, Olumide Akpata ya bayar
  • Har ila yau, LP ta zargi dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar, Peter Obi da jawo mata rashin nasara inda ta zo na uku

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Edo - Shugaban tsagin jam'iyyar LP, Julius Abure ya zargi faduwarsu a zaben kan ɗan takara, Olumide Akpata.

Abure ya kuma zargi dan takarar shugaban kasa, Peter Obi da ba da gudunmawa wurin kifar da jam'iyyar.

Kara karanta wannan

"An yi mana fashi da tsakar rana:" PDP ta soki sakamakon zaben gwamnan Edo

Jam'iyya ta zargi dan takararta kan faduwa zaben gwamnan
Tsagin jam'iyyar LP ta zargi faduwarta a zaben jihar Edo kan Peter Obi. Hoto: Peter Obi.
Asali: UGC

LP ta zargi Obi kan zaben Edo

Sakataren jam'iyyar Abayomi Arabambi shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da Vanguard ta samu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jam'iyyar ta kuma taya zababben gwamnan na jam'iyyar APC, Monday Okpebholo murnar yin nasara a zaben.

Jam'iyyar LP ta yabi zaben gwamnan Edo

Ta ce wannan zabe da aka yi na daga cikin mafi kyawu da kuma adalci ba tare da wasu kura-kurai ba.

"Duk abin da INEC ta yi daidai ne, matsalarmu da shugabanni shi ne duk lokacin da abu mai mana dadi ba, to ba shi da kyau."
"Amma idan kuma ya zo a yadda muke so to ko ba shi da kyau za mu iya cewa hakan ya na da kyau."

- Abayomi Arabambi

Jam'iyyar ta ce son mulki da yaudara da kuma cin amana na Peter Obi da Gwamna Alex Otti su ne musabbabin faduwarta a zaben da aka yi a ranar Asabar 21 ga watan Satumbar 2024.

Kara karanta wannan

Baki har kunne: Shugaban APC, Abdullahi Ganduje ya samu manyan nasarori a cikin mako 1

Zaben Edo: Dan PDP ya fashe da kuka

Kun ji cewa bayan sanar da sakamakon zaben jihar Edo, jam'iyyar PDP ta cigaba da kokawa kan yadda aka gudanar da zaben.

Mataimakin daraktan kamfen dan takarar PDP, Asue Ighodalo ya koka kan yadda aka tafka magudi a zaben da aka yi.

Emmanuel Odigie ya fashe da kuka ana tsaka da hira da shi a gidan talabijin inda jagoran shirin ya yi ta rarrashinsa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.