Edo 2024: Jerin Yan Takara 17 da Suke Neman Kujerar Gwamna

Edo 2024: Jerin Yan Takara 17 da Suke Neman Kujerar Gwamna

  • A ranar Asabar mai zuwa hukumar zaben mai zaman kanta ta sanar da cewa za a gudanar da zaben sabon gwamna a jihar Edo
  • Hukumar zabe mai zaman kanta ta tantance adadin yan takarar da za su fafata a zaben tare da mataimakansu a dukkan jam'iyyu
  • A wannan rahoton, Legit ta tatttaro muku adadin dukkan yan takarar, mataimakansu da wasu bayanai da suka shafe su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Edo - Shirye shirye sun kankama yayin da ake shirin gudanar da zaben gwamna a jihar Edo a ranar Asabar mai zuwa.

Yan takara 17 ne za su fafata daga jam'iyyu mabanbanta a zaben inda aka samu mace daya a cikinsu.

Kara karanta wannan

Olumide Akpata: Dan takarar LP mai barazana ga jam'iyyu a zaben Edo

Zaben Edo
Yan takarar gwamna a zaben Edo. Hoto: Okpebholo Monday| Akpata Olumide Anthony|Barista Ighodalo
Asali: Facebook

Jerin masu takarar gwamnan jihar Edo

Legit ta samo cikakken bayani kan yan takarar ne a cikin bayanin da hukumar INEC ta wallafa a shafinta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

  1. Jami'yyar A ta tsayar da Iyere Kennedy dan shekaru 50 matsayin dan takarar gwamna a jihar Edo inda Enanulele zai zama mataimakinsa.
  2. A jam'iyyar AA, Isegjohi Tom mai shekaru 60 da haihuwa ne zai yi takarar gwamnan kuma Onaiwu Mabel Osemwonye Nmwen ne mataimakinsa.
  3. Jami'yyar AAC ta tsayar da Udo Oberaifo David mai shekaru 37 a matsayin dan takarar gwamna yayin da Osunde Lord Osas zai zama mataimakinsa.
  4. A bangaren ADC kuma, Izedonmwen Osarenren Derek ne mai 47 zai yi takarar gwamna a Edo sai Osagie Philip mataimakinsa.
  5. Jam'iyyar ADP ta tsayar da Akhimie Kingson mai shekaru 37 a matsayin dan takarar gwamna sai kuma mataimakiyarsa mai suna Obazee Ramatu
  6. APC ta tsayar da Okpebholo Monday mai shekaru 53 a matsayin dan takarar gwamna sai kuma Idahosa Dennis a matsayin mataimakinsa.
  7. APGA ta tsayar da Osifo Isaiah mai shekaru 64 a matsayin dan takara sai Bello Aneru a matsayin mataimaki.
  8. Jam'iyyar APM ta tsayar da Ugiagbe Odaro Sylvester mai shekaru 45 a matsayin dan takarar gwamna sai Ezomo Timothy Ede a matsayin mataimaki.
  9. APP ta tsayar da tsayar da Areloegbe Amos Osalumese mai shekaru 56 sai kuma mataimakiyarsa Oyarenua Paul.
  10. BP ta tsayar da Osiriame Edeipo mai shekaru 47 takarar gwamna a Edo sai kuma mataimakiyarsa mai suna Omorogbe Kingsley.
  11. LP ta tsayar da Akpata Olumide Anthony mai shekaru 51 takarar gwamnan Edo sai mataimakiyarsa mai suna Alufohai Faith.
  12. NNPP ta tsayar da Azena Azemhe Friday mai shekaru 44 takarar gwamnan Edo sai mataimakiyarsa Isokpan Ihueghian.
  13. PDP ta tsayar da Barista Ighodalo Asuerinme mai shekaru 64 takarar gwamnan Edo sai kuma mataimakinsa mai suna Ogie Osarodion.
  14. Jam'iyyar PRP ta tsayar da Key Patience Ndidi mai shekaru 50 a matsayin yar takara sai mataimakinta Ojo Advice.
  15. SDP ta tsayar da Anerua Abdulai Aliu mai shekaru 53 a matsayin dan takara sai kuma mataimakinsa Ahmed Paul.
  16. YPP ta tsayar da Paul Ovbokhan mai shekaru 40 a matsayin dan takara da mataimakinsa Mustapha Ahmed Tijani.
  17. Jami'yyar ZLP ta tsayar da Akhlamhe Amiemenoghena mai shekaru 43 takarar gwamnan Edo sai mataimakiyarsa mai suna Idubor Joyce Olamilayo.

Kara karanta wannan

Hotuna: Yadda rundunar sojin sama ta fara jigilar kayan aikin zaben gwamnan Edo

Atiku ya yi gargadi kan zaben Edo

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya yi kira na musamman kan zaben gwamna da ake shirin yi a Edo.

Atiku Abubakar ya ce zaben APC a Edo zai kara mayar da jihar baya kuma hakan na nuni ne da cewa an zaɓi wahala a kan sauki.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng