‘Za Mu Yi Nasara duk da Ana Wahala:’ Jigon APC kan Zabe Mai Zuwa a Edo

‘Za Mu Yi Nasara duk da Ana Wahala:’ Jigon APC kan Zabe Mai Zuwa a Edo

  • Jigon jami'yyar APC ya ce wahalar rayuwa da ake fama da ita a Najeriya ba za ta saka yan Najeriya su juwa musu baya ba a Edo
  • Tsohon dan majalisa, Ehiozuwa Johnson Agabonayinma ya ce wahalar rayuwa da ake fama da ita ba laifin Bola Tinubu ba ne
  • Ɗan siyasar ya ce yan siyasa sun sace biliyoyin kudi a mulkin Muhammadu Buhari wanda hakan na cikin matsalolin ƙasar nan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Tsohon dan majalisar tarayya kuma jigo a jam'iyyar APC ya ce tsadar rayuwa ba za ta saka a juwa musu baya a zaben Edo ba.

Ehiozuwa Johnson Agabonayinma ya ce gwamnatin Bola Ahmed Tinubu tana kokari duk da matsin tattalin arziki da ake ciki.

Kara karanta wannan

An yi mummunan haɗari a ranar Maulidi, mutane kusan 20 sun kone kurmus

Zaben Edo
Jigon APC ya ce za su yi nasara a Edo. Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Twitter

Jaridar Vanguard ta wallafa cewa Ehiozuwa Johnson Agabonayinma ya ce APC ta kammala shirye shirye domin zaben Edo mai zuwa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wahalar rayuwa da zaben APC a Edo

Tsohon dan majalisar tarayya jihar Edo, Ehiozuwa Johnson Agabonayinma ya ce yana da tabbas a kan yan Najeriya ba za su juya musu baya a zaben gwamna a Edo ba.

Ehiozuwa Johnson ya ce yana da tabbas ne a kan cewa ba shugaban kasa Bola Tinubu ba ne ya jefa kasar cikin wahalar rayuwa a Najeriya.

Bayan haka, ya kara da cewa mutanen jihar Edo sun gaji da mulkin PDP a jihar saboda haka za su so dawowa karkashin APC domin samun cigaba.

An yi sata a mulkin Buhari inji Ehiozuwa

Ehiozuwa Johnson ya ce satar da aka yi a ƙarƙashin mulkin Muhammadu Buhari na cikin abubuwan da suka jefa Najeriya a wahalar rayuwa.

Kara karanta wannan

'Kowa na talaucewa' Malamin addini ya tura zazzafan sako ga Bola Tinubu

Saboda haka ya ce Bola Tinubu ya gaji Najeriya ne bayan an lalata abubuwa a zamanin Buhari wanda shi ma ya samu abubuwa ne a lalace.

A karshe, Ehiozuwa Johnson ya ce dole a tashi tsaye a yaki cin hanci da rashawa idan ana son kawo cigaba mai dorewa a Najeriya.

Edo: An kammala yakin neman zabe

A wani rahoton, kun ji cewa yayin da ake shirin gudanar da zaben Edo, an kawo karshen yakin neman zabe da aka yi na tsawon kwanaki a jihar.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da shugaban APC, Abdullahi Ganduje sun samu halartar yakin neman zaben inda suka nemi a marawa APC baya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng