Kebbi: APC Ta Mayar da Martani bayan Sanar da Sakamakon Zaben Kananan Hukumomi

Kebbi: APC Ta Mayar da Martani bayan Sanar da Sakamakon Zaben Kananan Hukumomi

  • Jam'iyyar APC mai mulki ta samu nasarar lashe dukkan kujerun shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli a jihar Kebbi
  • A ranar Asabar, 31 ga watan Agusta aka gudanar da zaɓen kananan hukumomi wanda PDP ta tsame kanta bisa zargin maguɗi
  • Jam'iyyar APC mai mulki ta ce zaɓen ya gudana cikin lumana babu tashin hankali kuma al'umma sun ba da haɗin kai wajen zaben

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kebbi - All Progressives Congress (APC) ta lashe zaɓen kananan hukumomin da aka gudanar a jihar Kebbi ranar Asabar da ta gabata.

Shugaban hukumar zaɓen jihar Kebbi mai zaman kanta, Hon Aliyu Muhammed Mera shi ne ya sanar da sakamakon a Birnin Kebbi.

Kara karanta wannan

APC ta samu gagarumar nasara a zaben kananan hukumomin jihar Kebbi

Tutar APC.
Jam'iyyar APC ta samu nasara a zaben kananan hukumomin jihar Kebbi Hoto: @OfficialAPC
Asali: Getty Images

Ya ce jam'iyyar APC ta samu nasarar lashe dukkan kujerun ciyamomi da mataimakansu da kuma kansiloli, kamar yadda Leadership ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

APC ta faɗi yadda zaben ya gudana

Sai dai a wata sanarwa da kakakin APC, Isah Abubakar Assalafi ya fitar, ya ce an gudanar da zaben cikin lumana a dukkanin kananan hukumomi 21 na jihar.

Ya ce al'umma sun ba da haɗin kai, sun fito rumfunan zaɓensu kuma sun jefa ƙuri'a ba tare da fuskantar wata tangarɗa ba.

Jam'iyyar APC ta musanta iƙirarin PDP

Isah Assalafi ya kuma yi watsi da ikirarin jam'iyyar PDP cewa an yi maguɗi a zaɓen, inda ya ce an tura jami'an tsaro kowane akwati, cibiyoyi da ofisoshin hukumar zaɓe.

Kakakin APC ya bayyana cewa kwararru sun sa ido kan yadda aka gudanar da zaɓen, wanda hakan alama ce da ke nuna an yi sahihi kuma ingantaccen zaɓe.

Kara karanta wannan

Katsina: Kotun ɗaukaka ƙara ta yanke hukuncin ƙarshe kan kujarar ɗan majalisar tarayya

Ya yaba da yadda mutane suka fito suka kaɗa kuri'unsu cikin lumana babu fargaba ko ta da yamutsi, kamar yadda PM News ya kawo a rahotonta.

Atiku na da damar tsayawa takara a 2027?

A wani rahoton kuma wani jigo a PDP, Glintstone Akinniyi ya yi bayanin yadda Atiku Abubakar zai iya lashe tikitin takarar shugaban ƙasa a 2027.

Akinniyi ya ce idan Atiku na son takara ya zama tilas ya fito ya nema, inda ya ƙara da cewa jam'iyyu ba su ba mutum takara sai ya nema.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262