Gwamna a Arewa Ya Duba Matsin da Ake Ciki, Ya Naɗa Mutane Sama da 1,000 a.Muƙamai

Gwamna a Arewa Ya Duba Matsin da Ake Ciki, Ya Naɗa Mutane Sama da 1,000 a.Muƙamai

  • Gwamna Ahmed Usman Ododo ya naɗa sababbin hadimai 1,192 waɗanda suka fito daga faɗin kananan hukumomin jihar Kogi
  • Sakatariyar gwamnatin Kogi, Dr. Folashade Ayoade ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta fitar, ta ce za su fara aiki ranar 1 ga watan Satumba
  • Waɗanda gwamnan ya naɗa sun haɗa da manyan mataimaka na musamman da mataimaka na musamman a gundumomi da kananan hukumomi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kogi - Gwamnan jihar Kogi, Alhaji Ahmed Usman Ododo, ya amince da nadin karin hadimai 1,192.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakatariyar gwamnatin jihar Kogi Dr Folashade Ayoade ta fitar a ranar Litinin, 19 ga watan Agusta, 2023.

Kara karanta wannan

Gwamnan Plateau ya dakatar da manyan jami'an gwamnati mutum 4

Ahmed Usman Ododo.
Gwamna Ahmed Ododo ya nada mutum 1,192 a matsayin hadimai a jihar Kogi Hoto: Alhaji Ahmed Usman Ododo
Asali: Facebook

Sanarwan ta ce Gwamma Ododo ya amince da naɗin Yakubu Abdulhakeem a matsayin babban sakataren hukumar kula da naƙasassu ta jihar Kogi, Punch ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna ya naɗa SSA da SA

Ahmed Ododo ya kuma naɗa manyan masu taimaka masa na musamman (SSA) 166 da kananan mataimaka na musamman (SA) 36.

Sanarwar ta ce:

"Hadiman da gwamna ya naɗa sun hada da Yakubu Abdulhakeem a matsayin Babban Sakatare, ofishin nakasassu na jihar Kogi, da manyan mataimaka na musamman 165, da mataimaka na musamman 36.
"Sauran waɗanda gwamnan ya naɗa sun haɗa da hadimai 574 na gundumomi da masu taimakawa na musamman 29 a kananan hukumomin jihar Kogi."

Ododo ya naɗa haɗimai a ofishin matarsa

Alhaji Ahmed Ododo ya kuma amince da nadin Alhaji Ibrahim Abdulsadiq a matsayin Darakta a ofishin uwar gidan gwamna da da wasu hadimai.

Kara karanta wannan

Matatar Ɗangote: Gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakin sauke farashin fetur a Najeriya

Gwamnan ya taya daukacin wadanda suka samu muƙamai murna, sannam ya buƙaci su yi iya bakin kokarinsu wajen yiwa al'umma hidima da kawo ci gaba a Kogi.

A ƙarshe sakatariyar gwamnatin ta ce dukkan waɗannan naɗe-naɗe za su fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Satumba, 2024.

Zaben Kogi: Kotun koli za ta raba gardama

A wani rahoton kuma kotun koli ta tanadi hukunci a karar da Murtala Ajaka dan takarar SDP ya shigar na kalubalantar nasarar Usman Ododo a zaben Kogi.

Ajaka ya daukaka kara kan hukuncin dakotun zabe ta yi na tabbatar da zaben Ahmed Usman Ododo na APC a matsayin gwamnan Kogi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262