Gwamna Zai Rabawa Matasa Kyautar Biliyoyin Naira Saboda ba Su Shiga Zanga Zanga ba

Gwamna Zai Rabawa Matasa Kyautar Biliyoyin Naira Saboda ba Su Shiga Zanga Zanga ba

  • Gwamnan jihar Ebonyi ya nuna farin ciki bisa yadda matasa suka masa biyayya, suka ƙi shiga zanga-zangar da aka fara a Najeriya
  • Francis Nwifuru ya bayyana cewa gwamnati ta ware N1.3bn domin rabawa matasa 1,300 tallafin da za su kama sana'a su dogara da kansu
  • Gwamnan ya ce wannan na ɗaya daga cikin abubuwan zai yi wa matasan Ebonyi domin nuna godiya da biyayyar da suka masa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ebonyi - Gwamnan jihar Ebonyi Francis Nwifuru ya ce a yunkurinsa na rage radadin da matasa ke ciki da sa su dogaro da kansu, gwamnatinsa za ta tallafawa matasa 1,300.

Gwamna Nwifuru ya ce zai rabawa matasa 1,300 da suka fito daga ƙananan hukumomi 13 na jihar Ebonyi tallafin N1.3bn domin su faɗaɗa kasuwancinsu.

Kara karanta wannan

Gwamna ya gama shiri, zai fara biyan ma'aikata sabon albashi ana tsaka da zanga zanga

Gwamna Francis Nwifuru na jihar Ebonyi.
Zanga-zanga: Gwamnatin Ebonyi za ta tallafawa matasa 1,300 da N1.3bn Hoto: Francis Nwifuru
Asali: Facebook

Francis Nwifuru ya fadi haka ne a wurin taron raba tallafi na ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Ebonyi/Ohaukwu a garin Akpu Ngbo, kamar yadda Leadership ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna zai rabawa matasa N1.3bn

Ya ƙara da cewa zai rabawa matasan waɗannan maƙudan kuɗin ne saboda farin cikin biyayyar da suka masa a lokacin da ya nemi su kaucewa zanga-zangar da ake yi.

”Matasan mu sun nuna cewa suna da ɗa'a da biyayya ta hanyar amincewa da rokon da na yi masu na kada su shiga zanga-zangar nan domin amfanin jihar Ebonyi.
"Ba zaku biyo ni bashin rantsuwa ba, na yi maku alƙawarin cewa zan ci gaba da tallafa maku ta yadda za ku riƙa samun damarmaki a rayuwarku.

Ebonyi: Gwamna ya ba da kwangilar titi

Gwamnan ya shaida wa al'umma cewa tuni ya bayar da kwangilar gina titin Umuoguduosha- NigerCem mai tsawon kilomita 24.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Sojojin Najeriya sun yi magana kan kifar da gwamnatin Bola Tinubu

A cewarsa, ya ba da aikin ne ga ‘yan kwangila guda biyu domin tabbatar da kammala aikin cikin watanni 18, rahoton The Nation.

Kano: An kama masu hannu a ɗaga tutar Rasha

Kuna da labarin jami'an hukumar tsaron farin kaya DSS sun cafke masu ɗaukar nauyin telolin tutar ƙasar Rasha a jihar Kano da ke Arewa maso Yamma.

Tun farko dai jami'an tsaron sun kama telolin da ke ɗinka tutar a ranar Litinin bayan masu zanga-zanga sun fara ɗaga tutocin a kan titi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262