Ana Cikin Tsadar Rayuwa, Gwamma Zai Rushe Sabon Gidan Gwamnatin Biliyoyin Naira

Ana Cikin Tsadar Rayuwa, Gwamma Zai Rushe Sabon Gidan Gwamnatin Biliyoyin Naira

  • Gwamna Alex Otti ya bayyana shirinsa na rushe sabon gidan gwamnatin jihar Abia da ke Kudu maso Gabashin Najeriya
  • Tsohon gwamnan jihar, Okezie Ikpeazu ne ya karasa ginin da ya gada kuma ya kaddamar da shi ana gobe zai miƙa mulki a 2023
  • Tun bayan rantsar da shi a watan Mayu, Gwamna Otti ya koma garinsu yana tafiyar da harkokin gwamnatin jihar Abia

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Abia - Gwamna Alex Otti na jihar Abia ya sha alwashin rusa sabon gidan gwamnati da aka gina na biliyoyin Naira a babban birnin Umuahia.

Gwamna Otti ya bayyana hakan ne ranar Asabar a lokacin da yake bude sabon ofishin shugaban karamar hukumar Arochukwu da ke jihar Abia.

Kara karanta wannan

Ana harin zanga zanga gwamnati ta amince da ba da aikin da zai lakume N81bn

Gwamna Alex Otti na jihar Abia.
Gwamna Alex Otti ya bayyana shirinsa na rushe sabon gidan gwamnatin jihar Abia Hoto: Alex Otti
Asali: Facebook

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Ukoha Njoku, ya aikawa jaridar Premium Times ranar Lahadin da ta gabata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun bayan hawa kan madafun iko, Gwamna Otti ya kauracewa sabon gidan gwamnatin, inda ya koma mahaifarsa yana tafiyar da mulki daga can.

Yadda aka gina gidan gwamnatin Abia

Tsohon gwamnan jihar Okezie Ikpeazu, ne ya kaddamar da sabon gidan gwamnatin ranar 28 ga watan Mayu, 2023 kwana daya kafin sauka daga mulki.

Gwamna Ikpeazu ya gaji aikin daga magabacinsa,Theodore Orji, wanda ya sa harsashin ginin har zuwa matakin rufi.

Babu taƙamaiman kudin da aka kashe amma wata sanarwa da gwamnatin Abia ta fitar a ranar 29 ga Oktoba, 2012 ta nuna cewa ta biya Naira miliyan 175 na yin katanga kaɗai.

Gwamna Otti zai rushe katafaren ginin

Kara karanta wannan

Abba ya tura sunan Manjo Janar Majalisa domin tantance shi a matsayin kwamishinan Kano

A wurin buɗe sabon ofishin ciyaman a Arochukwu ranar Asabar, Gwamna Otti ya ce gwamnatinsa za ta "rushe" sabon gidan gwamnati kafin karshen shekarar nan.

Alex Otti ya ce zai sake gina wani “gidan gwamnati da ya dace a Abia," nan gaba bayan rushe na yanzu, kamar yadda Tribune ta rahoto.

"Ina sanar da ku cewa kafin ƙarshen shekarar nan zamu rusa lalatattun gine-ginen (gidan gwamnatin) kuma zamu yi sabo wanda ya dace da al'ummar jihar Abia."

Gwamna Buni ya rufe makarantun Yobe

A wani rahoton kuma Gwamnatin Yobe ta umarci rufe duka makarantun firamare da sakandire na jihar saboda zanga-zangar da ake shirin yi.

Kwamishinan ilimi a matakin farko, Abba Idriss Adam ne ya sanar da haka a Damaturu, babban birnin jihar Yobe da ke Arewa maso Gabas.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262