Jam'iyyar APC Ta Fara Zawarcin Mataimakin Gwamnan PDP, Za Ta Kafa Tuta a Ofishinsa

Jam'iyyar APC Ta Fara Zawarcin Mataimakin Gwamnan PDP, Za Ta Kafa Tuta a Ofishinsa

  • Jam'iyyar APC ta fara zawarcin mataimakin gwamnan jihar Edo, Philip Shaibu bayan harin da aka kai masa a filin jirgin sama
  • Shugaban APC na jihar Edo, Jarret Tenebe ya ziyarci Shaibu kuma ya buƙaci ya jefar da PDP saboda yunƙurin ɗaukar ransa
  • Kwamared Shaibu ya yabawa Tenebe bisa yadda yake ƙara masa kwarin guiwa, inda ya ƙara jaddada goyon bayansa ga APC

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Edo - Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta ci gaba zawarcin mataimakin gwamnan jihar Edo, Philip Shaibu bayan kotu ta maida shi kan muƙaminsa.

Shugaban APC reshen jihar Edo, Jarrett Tenebe ya yi kira ga Kwamared Shaibu ya jefar da ƙwallon mangwaro ko ya huta da ƙuda kana ya dawo cikin APC.

Kara karanta wannan

Tsohon shugaban PDP ya fusata da yadda wasu ke 'satar' kudi, ya fice daga jam'iyyar

Philip Shaibu.
Jam'iyyar APC ta fara kokarin jawo hankalin Philip Shaibu da baro PDP a Edo Hoto: @HonPhilipshaibu
Asali: Twitter

Tawagar APC ta ziyarci Shaibu

Mista Jarrett Tenebe ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya ziyarci Shaibu a gidansa da ke Benin, babban birnin jihar Edo ranar Jumu'a, Vanguard ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tenebe, wanda ya samu rakiyar wasu kusoshin APC, ya bayyana harin da aka kaiwa Shaibu a filin jirgin sama a matsayin wani yunƙuri na ɗaukar rayuwarsa.

"Abin da (ake zargin) jam'iyyar ka ta shirya shi ne ta ɗauki rayuwarka. A halin da muke ciki yanzu kai ne sahihin mataimakin gwamna a jihar Edo.
"Na kawo maka saƙon APC kuma daga yanzu tutarmu za ta fara kaɗawa a ofishinka,” in ji Tenebe.

Philip Shaibu ya yabawa shugaban APC

A nasa jawabin, Philip Shaibu ya yabawa shugaban APC kan yadda a koda yaushe yake kara masa kwarin gwiwa tun lokacin da ya tsinci kansa a rigima a jam’iyyar PDP.

Kara karanta wannan

Mataimakin gwamna ya tsokano rigima, ya faɗi gwamnan PDP da ya yi yunƙurin kashe shi

A cewarsa, wannan matakin kulawa shine abin da ake bukata a kowane irin shugabanci, kamar yadda Daily Nigerian ta kawo.

"Shugaban jam’iyyar PDP bai taba ɗaga waya ya kirani ko ya yi kokarin warware rikicin da ke faruwa ba duk da na nuna cewa ni dan jam’iyya ne.
"Da yardar Allah Sanata Monday Okpebholo da Dennis Idahosa na jam'iyyar APC ne za su zama gwamna da mataimakinsa a jihar Edo," in ji Shaibu.

Shaibu ya caccaki Gwamna Obaseki

A wani rahoton kuma Kwamared Philip Shaibu ya zargi Gwamna Godwin Obaseki da yunƙurin hallaka shi a hanyar dawowarsa jihar Edo ranar Alhamis.

Mataimakin gwamnan wanda kotu ta mayar kan muƙaminsa ya shigar da ƙara yana neman gwamnan da hadimansa su biya diyyar N5bn.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262