Ganduje Ya Buƙaci Sanata Ya Fice Daga APC Mai Mulki Ya Koma Jam'iyyar Adawa

Ganduje Ya Buƙaci Sanata Ya Fice Daga APC Mai Mulki Ya Koma Jam'iyyar Adawa

  • Jam'iyyar APC ta shawarci sanata mai wakiltar Borno ta Kudu, Muhammed Ali Ndume ya sauya sheka zuwa wata jam'iyyar adawa
  • Hakan ya biyo bayan sauke Ndume daga matsayin mai tsawatarwa a majalisar dattawa sakamakon sukar da ya yiwa Bola Tinubu
  • Tun farko Sanata Ndume ya soki gwamnatin Bola Tinubu inda ya yi iƙirarin cewa an rufe duk wata ƙofa ta ganin shugaban ƙasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Jam'iyyar APC mai mulki ta sauke Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta Kudu daga matsayin babban mai tsawatarwa a majalisar dattawan Najeriya.

Hakan na kunshe ne a wata takardar da jam'iyyar APC ta aika majalisar dattawan mai ɗauke da sa hannun shugaban jam'iyya, Abdullahi Ganduje da sakatare.

Kara karanta wannan

Muhimman abubuwa 6 game da Sanatan da ya karɓi matsayin Ndume a Majalisa

Sanata Ali Ndume.
Bayan sauke shi daga muƙamin majalisa, APC ta nemi Muhammad Ali Ndume ya koma wata jam'iyyar Hoto: Sen Muhammed Ali Ndume
Asali: Facebook

Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ne ya karanta takardar a zaman sanatoci na yau Laraba, 17 ga watan Yuli, 2024, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

APC ta buƙaci Ndume ya sauya sheƙa

A cikin takardar, APC ta bukaci Sanata Ndume ya tattara kayansa ya bar jam'iyya mai mulki, ya koma jam'iyyar da ya ga dama, Daily Trust ta kawo labarin.

Bugu da ƙari, jam'iyyar APC ta bayyana cewa ta ɗauki wannan matakin ne biyo bayan caccakar da Ndume ya yi wa gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Idan ba ku manta ba a wata hira da ya yi kwanan nan, Muhammed Ali Ndume ya soki gwamnatin Tinubu, inda ya yi ikirarin cewa hadimai sun babbake komai.

Silar fadan Sanata Ndume da APC

Kara karanta wannan

Majalisar Dattawa ta tsige sanatan APC daga muƙaminsa, ta maye gurbinsa nan take

Sanata Ali Ndume ya kuma koka kan cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta rufe dukkan kofofin da za a rika fada mata gaskiya kan halin da ake ciki.

Wannan kalamai ba su yi wa APC da wasu sanatoci daɗi ba, wanda hakan ya sa jam'iyyar ta sauke shi daga matsayin mai ladabtarwa a majalisa.

APC ta kuma ɓa shi shawarar cewa zai iya ficewa daga APC ya koma wata jam'iyya daga cikin jam'iyyun adawa.

Majalisa ta gano yadda ake asarar $9bn

A wani rahoton kuma Majalisar wakilai ta bayyana takaici kan yadda kasar nan ke tafka asara kan hakar ma'adanai ba bisa ka'ida ba.

Shugaban kwamitin ma'adanai, Hon. Jonathan Gbefwi ya ce ana asarar akalla $9bn duk shekara, wanda hakan ba karamar asara ba ce

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262