Ganduje Ya Cika da Murna Bayan Ya Yiwa PDP Wata Babbar Illa

Ganduje Ya Cika da Murna Bayan Ya Yiwa PDP Wata Babbar Illa

  • Shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Alhaji Umar Abdullahi Ganduje ya bayyana farin cikinsa kan shigowar Sanata Anyim Pius Anyim zuwa jam'iyyar
  • Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana shigowar tsohon shugaban na majalisar dattawa a matsayin babban alheri
  • Ya bayyana cewa za anba shi dama kamar sauran tsofaffin ƴaƴan jam'iyyar domin ya zo ya bayar da irin ta sa gudunmawar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana shigowar tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Pius Anyim zuwa jam’iyyar a matsayin "babban alheri".

Ganduje ya nuna murnarsa ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaransa, Mista Edwin Olofu, ya fitar.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar APC ta caccaki Sanata Ndume kan sukar Shugaba Tinubu

Ganduje ya yi murna kan dawowar Anyim Pius zuwa APC
Ganduje ya yi maraba da dawowar Sanata Anyim Pius Anyim zuwa APC Hoto: @Naija_PR
Asali: Twitter

Me Ganduje ya ce kan dawowar Anyim zuwa APC

Sanarwar wacce aka fitar a ranar Lahadi a Abuja, ta ruwaito Ganduje na faɗin cewa, ƙwarewar Sanata Anyim za ta yi amfani ga jam'iyyar APC, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun da farko Ganduje ya karɓi Sanata Anyim wanda ya sauya sheƙa daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC yayin wani taron yaƙin neman zaɓe a Abakaliki babban birnin jihar Ebonyi.

"Na yi farin cikin tarbar wannan muhimmin mutumin zuwa cikin jam'iyyar mu."
"Ina son na ba ka tabbaci a madadin shugaban ƙasa Bola Tinubu, cewa muna maka maraba da zuwa babbar jam'iyyar siyasa a nahiyar Afirika."
"Ina ba ka tabbacin cewa za a ba ka dama kamar yadda aka ba tsofaffin mambobin jam'iyyar mu ta yadda za ka ba da taka irin gudunmawar."

Kara karanta wannan

APC ta yi babban kamu, tsohon shugaban majalisar dattawa ya koma jam'iyyar

- Abdullahi Umar Ganduje

Jaridar Vanguard ta ce shugaban na jam'iyyar APC ya kuma buƙaci yankin Kudu maso Gabashin Najeriya da bar jam'iyyar adawa ya shigo a dama da shi a jam'iyya mai mulki.

APC ta caccaki Sanata Ali Ndume

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta caccaki Sanata Ali Ndume bisa kalaman da ya yi kan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

APC ta bayyana cewa kalaman Ndume na cewa ba a ganin shugaban ƙasan kuma bai san halin da ake ciki a ƙasar nan ba, ba su dace ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng