Gwamna Ya Faɗi Sunan Wanda Ya Tayar da Bam, Ya Alakanta Shi da Ministan Tinubu

Gwamna Ya Faɗi Sunan Wanda Ya Tayar da Bam, Ya Alakanta Shi da Ministan Tinubu

  • Gwamna Siminalayi Fubara ya bayyana sunan wanda ya tashi bam da nufin kara tayar da hargitsi a jihar Ribas lokacin zanga-zanga
  • Sakataren yaɗa labaran gwamnan, Nelson Chukwudi ya ce mutumin, Josiah Preye ya kammala karatun Jami'a kuma ɗan tsagin Wike ne
  • Ya kuma kafa hujja da faifan bidiyon wanda ake zargin a cikin masu zanga-zanga da kuma lokacin da yake jinya a asibiti

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Rivers - Gwamnatin jihar Ribas karkashin Gwamna Siminalayi Fubara ta bayyana sunan wanda ake zargi da tayar da bam a Fatakwal a ranar Talata.

Gwamnatin ta bayyana sunansa da Josiah Preye, wanda ya kammala karatu a jami'a kuma yana rayuwa gami da aiki a Fatakwal, babban birnin jihar.

Kara karanta wannan

Rikicin sarauta da shari’ar zabe ba su taka masa burki ba, an nada Abba gwarzon Gwamnoni

Gwamna Siminalayi Fubara.
Gwamnatin Fubara ta jaddada cewa wanda ake zargi da tayar da bam ɗan tsagin Wike ne Hoto: Sir Siminalayi Fubara
Asali: Facebook

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaran Gwamna Fubara, Nelson Chukwudi ya fitar, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Siminalayi Fubara ya jaddada cewa wanda ake zargi da yunkurin tayar bam ɗin ɗan tsagin ministan babban birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike ne.

Yadda lamarin ya faru a Rivers

Idan ba ku manta ba, wani abin fashewa ya tashi a kusa da katafaren otal a Fatakwal a lokacin da ake zanga-zanga kan canza shugabannin ƙananan hukumomi a Fatakwal.

Sai dai rahotanni sun nuna cewa abun fashewar ya tashi da wanda ake zargin tun kafin ya ida nufinsa, kuma yanzu haka jami'an tsaro na tsare da shi a asibiti.

Bayan haka ne Gwamna Fubara ya fito ya ɗora laifin kan magoya bayan Wike, inda ya ce sun shirya tayar da bam din ne domin a ayyana dokar ta ɓaci a jihar, Premium Times ta rahoto.

Kara karanta wannan

Gwamnan Kano ya ware N4.8bn domin gyara makarantu, mutane 17, 000 za su samu aiki

Fubara ya saki bayanan wanda ake zargi

Sanarwar da sakataren yaɗa labaran gwamnan ya fitar ta yi bayanin cewa wanda ake zargin na cikin masu zanga-zangar goyon bayan Wike a ranar Talata.

Gwamnatin Fubara ta kafa hujja da faifan bidiyon wani a cikin masu zanga-zanga rufe da fuska wanda ta ce shi ne wanda ake zargi da bidiyon wanda ke jinya a asibiti.

Gwamna Fubara ya soki PDP

A wani rahoton kuma Gwamna Siminalayi Fubara ya bayyana rashin jin dadinsa ga jam'iyyar PDP inda ya ce ta gaza a jihar Rivers.

Gwamna Fubara ya bayyana cewa jam'iyyar PDP ta gaza wajen cimma muradunsa da magoya bayansa a jihar da ke Kudancin Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel