Bukatar Bola Tinubu Ta Jawo Zazzafar Muhawara a Majalisar Tarayya, Hayaniya Ta Ɓarke

Bukatar Bola Tinubu Ta Jawo Zazzafar Muhawara a Majalisar Tarayya, Hayaniya Ta Ɓarke

  • Ƴan majalisar wakilan tarayya sun yi zazzafar muhawara a tsakaninsu kan buƙatar da Bola Tinubu ya aiko ranar Alhamis, 27 ga watan Yuni, 2024
  • Mambobin majalisar sun tafka zazzafan kace-nace kan buƙatar Tinubu na tsawaita lokacin aiwatar da kasafin 2023 zuwa watan Disamba
  • Shugaban marasa rinjaye na majalisar, Kingsley Chinda, ya ce ba daidai ba ne a ce kasar nan na tafiyar da kasafin kudi uku zuwa hudu a lokaci guda

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Buƙatar da shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya tura majalisar wakilai ta haifar da zazzafar muhawara a zaman yau Alhamis, 27 ga watan Yuni, 2024.

Shugaba Tinubu ya buƙaci majalisar ta tsawaita wa'adin aiwatar da kasafin 2023 na N23.83trn da ƙarin kasafin 2023 na N2.17 zuwa watan Disamba.

Kara karanta wannan

Yajin aiki: ASUU ta fadi matakin da ta dauka bayan ganawarta da gwamnatin tarayya

Majalisar wakilai.
An yi mahara mai zafi kan bukatar Bola Tinubu a majalisar wakilan tarayya Hoto: House Of Representatives
Asali: Facebook

Buƙatar Tinubu ta tayar da hayaniya

Sai dai kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, lamarin bai kwanta ma shugaban marasa rinjaye, Kingsley Chinda ba, nan take ya tashi ya nuna damuwarsa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Honorabul Chinda ya nuna damuwa da cewa a hankalce ba daidai ba ne a ce ƙasa ta tasa kasafin kuɗi guda uku zuwa huɗu tana aiwatar da su a lokaci guda.

Dan majalisar PDP daga jihar Ribas ya bada shawarar cewa maimakon tsawaita lokacin, kamata ya yi a ɗauki muhimman ayyuka da ke cikin karin kasafin a haɗe su a babban kasafin 2023.

Tajudeen ya ɗauki mataki

Duk da rokon da kakakin majalisar Abbas Tajudeen ya yi, yawancin ‘yan majalisar sun nuna ba su yarda da tsawaita kasafin ba, inda suka ci gaba da nanata a'a.

A rahoton Premium Times, mambobin jam'iyyun adawa sun tayar da hayaniya domin hana kakakin majalisar Tajudeen shawo kan lamarin.

Kara karanta wannan

Shettima ya sa labule da gwamnoni kan sabon mafi ƙarancin albashi da wasu batutuwa

Daga nan Tajuddeen ya ayyana shiga zamam sirri domin ƴan majalisar su fahimci lamarin kuma su warware batutuwan kafin ci gaba da duba kudirori.

Shettima da gwamnoni sun sa labule

A wani rahoton na daban Sanata Kashim Shettima da gwamnoni sun sa labule a fadar shugaban kasa da ke Abuja kan muhimman batutuwa.

Mataimakin shugaban ƙasar ne ke jagorantar taron wanda ke gudana karkashin majalisar tattalin arzikin ƙasa (NEC).

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel