A Karshe, Shugaba Tinubu Ya Sansanta Ricikin Minista da Gwamnan PDP Kan Sharuɗda 8

A Karshe, Shugaba Tinubu Ya Sansanta Ricikin Minista da Gwamnan PDP Kan Sharuɗda 8

  • Bola Ahmed Tinubu ya warware rikicin siyasar da ya shiga tsakanin Gwamna Fubara na Ribas da ministan Abuja, Nyesom Wike
  • A taron neman maslaha da ya gudana a Villa, Wike da Gwamna Fubara sun rattaba hannu kan yarjejeniya mai kunshe da abu takwas
  • Gwamna Fubara da uban gidansa a siyasa sun samu saɓani ne tun lokacin da majalisar dokokin Ribas ta yi yunkurin tsige shi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - A karshe, shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya samu nasarar lalubo bakin zaren da zai kawo karshen dambarwar siyasar da ta ɓarke a jihar Ribas.

Yayin zaman sulhu da masu ruwa da tsakin jihar Ribas, Bola Tinubu ya kama hanyar warware saɓanin da ya shiga tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da ministan Abuja, Nyesom Wike.

Kara karanta wannan

Tinubu ya fara tunanin ɗauko tsohon ministan Buhari ya maye gurbin Lalong, ya gana da jiga-jigai 2

An lalubo bakin zaren rikicin Ribas.
A karshe, Shugaba Tinubu, Gwamna Fubara da Wike Sun Cimma Matsaya Uku a Villa Hoto: Sir Siminalayi Fubara, Bola Tinubu, Nyesom Wike
Asali: Facebook

A wata sanarwa da hadimin shugaban ƙasa ya wallafa a Twitter, Tinubu ya yi taron sirri da Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas, Peter Odili da wasu jiga-jigai domin warware matsalar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Fubara, wanda ya halarci zaman a fadar shugaban ƙasa, ya rattaba hannu kan yarjejeniya tare da yan majalisar dokokin jihar da suka sauya sheƙa zuwa APC.

Fubara zai janye kararrakin da ya shigar kotu

Gwamnan ya kuma amince zai janye dukkan kararrakin da ya shigar gaban kotu kan ƴan majalisar masu goyon bayan Wike da suka sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

Haka nan kuma majalisar dokokin jihar Ribas ta amince zata dakatar da duk wani yunƙuri na tsige Gwamna daga kan madafun iko.

Ƙarin wata matsayar da aka cimmawa a taron sasancin ita ce barin ɓangaren majalisa su yi aikinsu ba tare da yi masu katsalandan ba.

Kara karanta wannan

Tinubu ya saka labule da gwamnan PDP da kuma tsohon gwamna, an fadi dalili

Tsagin Wike da tsagin Fubara duk sun aminta cewa gwamnan ba zai sake tsoma baki kan harkonin majalisa ba yayin da su kuma ƴan majalisar za a basu daman yin zamansu duk suke so.

Fubara ya kuma yarda cewa zai sakar wa majalisar dukkan kuɗaɗenta kuna ba zai tsoma baki kan yadda majalisar zata kashe kuɗin ba.

Shugaba Bola Tinubu Ya Sa Labule da Wakilan NPAN

A wani rahoton na daban Bola Ahmed Tinubu na ganawa da wakilan kungiyar gidajen jaridu ta ƙasa (NPAN) a fadarsa da ke birnin tarayya Abuja.

Shugaban kamfanin jaridar Daily Trust kuma shugaban NPAN na ƙasa, Malam Kabiru Yusuf, ne ya jagoranci tawagar zuwa Villa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel