Allah Ya Yi Wa Shehu Othman Rasuwa Yana Da Shekara 91

Allah Ya Yi Wa Shehu Othman Rasuwa Yana Da Shekara 91

  • Iyalan tsohon kwamishinan jihar Benue, Alhaji Shehu Othman, sun shiga gagarumin jimami sakamakon rasuwarsa
  • Iyalansa sun tabbatar da lamarin cikin wata sanarwa a ranar Laraba, 29 ga watan Nuwamba, suna mai cewa ya rasu bayan gajeruwar rashin lafiya
  • Marigayin ya rike mukamai da dama a gwamnatin tsohuwa jihar Benue-Plateau, da kuma wasu mukaman a hukumomin tarayya daban-daban

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aminu Ibrahim ya shafe fiye da shekaru 5 yana kawo rahotanni kan siyasa, al'amuran yau da kulum, da zabe

FCT, Abuja - An tabbatar da rasuwar tsohon kwamishina a tsohuwar jihar Benue, Alhaji Shehu Othman. Dan siyasan ya rasu yana da shekaru 91 a duniya.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta rahoto, Othman ya rasu a ranar Laraba, 29 ga watan Nuwamba, a Asibitin Trust Charitos da ke Jabi, a Abuja bayan gajeruwar rashin lafiya.

Kara karanta wannan

Yanzu: Bakin ciki yayin da tsohon Gwamnan Anambra, Ezeife, Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Shehu Othman
Najeriya ta yi rashin wani babban dan siyasa, Shehu Othman. Hoto: Shehu Othman
Asali: Facebook

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Iyalan Othman sun tabbatar da rasuwarsa cikin wata sanarwa suka kuma nuna cewa za a birne dan siyasan a ranar da ya rasu bayan sallar azahar a Babban Masallacin Abuja.

Iyalan sun rubuta:

"Inna lillahi wa ina ilaihi raji un.
"Za a yi jana'iza bayan sallar Azahar (1.30pm) a Masallacin Kasa na Abuja.
"Sannan za a birne shi a Makabartar Gudu bayan masa sallah."

An haifi Othman ne a ranar 26 ga watan Yuni, kuma shi da ke sarautar Magajin Garin Keana kafin rasuwarsa.

Malami a OAU ya fadi matacce a ofishinsa

Tunda farko, Legit ta rahoto cewa wani lakcara a Jami'ar Obafemi Awolowo (OAU) da ke Ile-Ife a jihar Osun ya fadi ya kuma ce ga garinku a ofishinsa, jaridar The Sun ta rahoto.

Marigayin, wanda aka ce sunansa Dr Ayo Ojediran, ya koyar a Sashin Kimiyya da Fasahar Ilimi, Tsangayar Ilimi a makarantar.

Kara karanta wannan

Jerin mutane 8 da suka bada taimakon miliyan 700 da aka kashe masu Maulidi a Tudun Biri a Kaduna

An tsinci gawar malamin a ofishinsa a ranar Talata, 14 ga watan Nuwamba, yayin da wasu abokan aikinsa suka shiga ofishin.

Tsohon minista Musa Gwadabe ya rasu

A wani rahoton kun ji cewa tsohon Ministan Kwadago kuma jigo a jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Alhaji Musa Gwadabe ya riga mu gidan gaskiya.

Rahotanni sun bayyana cewa Gwadabe ya rasu a ranar Laraba 26 ga watan Afrilu yayin da ya ke da shekaru 87 a duniya. Ya mutu bayan gajeruwar rashin lafiya a wani asibiti a Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164