Kotun Daukaka Ƙara Ta Yanke Hukunci Kan Nasarar Ɗan Majalisar Tarayya Bayan Kotu Zaɓe Ta Tsige Shi

Kotun Daukaka Ƙara Ta Yanke Hukunci Kan Nasarar Ɗan Majalisar Tarayya Bayan Kotu Zaɓe Ta Tsige Shi

  • Bayan Kotun zaɓe ta soke nasararsa, ɗan majalisar tarayya na LP daga Legas ya samu nasara a Kotun ɗaukaka ƙara
  • Kotun ta jingine hukuncin farko, kana ta tabbatar da Thaddeus Attah a matsayin sahihin ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Eti Osa a Legas
  • Kwamitin Kotun ɗaukaka ƙara ya ce shaidun da ƙaramar Kotu ta dogara da su ba su inganta ba

Ahmad Yusuf, kwararren Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos - Kotun ɗaukaka ƙara ta sake tabbatar da nasarar Mista Thaddeus Attah na Labour Party a matsayin ɗan majalisar wakilan tarayya mai wakiltar mazaɓar Eti Osa a jihar Legas.

Mista Thaddeus Attah na LP.
Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar da Nasarar Dan Majalisar Tarayya Na LP a Legas Hoto: @thecable
Asali: Twitter

A baya Kotun sauraron korafe-ƙorafen zaben ƴan majalisar tarayya da na jiha mai zama a Tafawa Balewa Square, jihar Legas ta rushe nasarar Otta, kamar yadda Premium Times ta tattaro.

Kara karanta wannan

Kotun ɗaukaka ƙara ta raba gardama, ta yanke hukunci kan nasarar Gwamanan PDP

Amma a ranar Alhamis, 9 ga watan Nuwamba, 2023, Kotun daukaka ƙara ta jingine hukuncin Kotun zaɓen kana ta maida wa Otta kujerarsa ta ɗan majalisar tarayya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa ta soke hukuncin Kotun zaɓe?

Kwamitin alkalai uku na Kotun ya aminta da bayanan lauyan ɗan majalisar, Mike Ozekhome (SAN) cewa Kotun zaɓen ta yi kuskure a hukuncin da ta yanke.

Kotun ɗaukaka ƙarar ta gamsu cewa ƙaramar Kotun ta yi kuskure yayin da ta dogara da takardun da wasu shaidu, waɗanda ba wakilan jam'iyya ba, suka gabatar mata.

Ta bayyana cewa shaidun sun bayyana ne kawai a gaban kotun don gabatar da Fam EC8A (takardun sakamakon zabe a rumfuna) wanda ba su da alaƙa da shi.

Kotun ta ce bai kamata kotun zaɓe ta dogara da shaidar shaidun ba wajen tantance gaskiyar runfunan da aka gudanar da zabe ko aka soke zabe ba.

Kara karanta wannan

To Fa: Ana jajibirin zaɓe, Ɗan takarar Gwamna na jam'iyyar APC ya sha da ƙyar, bayanai sun fito

Bisa haka ta yanke cewa saɓanin hukuncin ƙaramar Kotu, zaben da aka gudanar a mazaɓar ya kammala, kana ta soke umarnin INEC ta shirya sabon zaɓe ciko cikin kwanaki 90.

Daga nan Kotun ɗaukaka ƙara ta soke hukuncin Kotun zaɓe kana ta tabbatar wa ɗan Majalisar da kujerarsa ta mamba a majalisar wakilan tarayya, The Cable ta ruwaito.

Kotu ta yi hukunci kan zaben jihar Akwa Ibom

A wani labarin na daban Kotun ɗaukaka ƙara ta yanke hukunci kan ƙarar da jam'iyyu biyu suka kalubalanci nasarar Gwamna Eno na Akwa Ibom

Yayin yanke hukunci ranar Jumu'a, Kotun ta kori ƙarar AA da AP bisa rashin cancanta, ta amince da hukuncin Kotun zaɓe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262