"Kotun Ƙoli Ba Ta Tabbatar da Nasarar Tinubu a Zaben 2023 Ba" Datti Ya Faɗi Abu 1 da Kotun Ta Yi

"Kotun Ƙoli Ba Ta Tabbatar da Nasarar Tinubu a Zaben 2023 Ba" Datti Ya Faɗi Abu 1 da Kotun Ta Yi

  • Ranar Litinin 6 ga watan Nuwamba, Peter Obi ya gudanar da taron manema labarai kan hukuncin Kotun ƙoli da ya tabbatar da nasarar Tinubu
  • Yayin da Obi ya jaddada cewa yanzu aka fara, abokin takararsa, Datti Baba-Ahmed ya kafe kan cewa ba Tinubu ne ya ci zaɓen 2023 ba
  • Obi da Datti sun caccaki Kotun kolin Najeriya da zargin cewa ta sauka daga tsarin da aka kafa Kotunan doka

Ahmad Yusuf, gogaggen Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a inuwar LP a zaɓen 2023, Dakta Yusuf Datti Baba Ahmed, ya yi martani kan hukuncin Kotun kolin Najeriya.

Shugaba Tinubu da Yusuf Datti Baba Ahmed.
"Kotun Koli Ba Ta Ayyana Tinubu a Matsayin Wanda Ya Ci Zabe Ba" Datti Ya Magantu Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Datti Baba-Ahmed
Asali: Facebook

Datti Baba-Ahmed ya ce Kotun ƙolin Najeriya ba ta ayyana shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin sahihin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2023 ba.

Kara karanta wannan

Nasarar Tinubu: Peter Obi ya yanke shawara kan sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2027

Abokin takarar Obi ya kafe Tinubu bai ci zaɓe ba

Ya yi wannan furucin ne a wurin taron manema labaran da suka gudanar ranar Itinin, 6 ga watan Nuwaba, 2023 kan hukuncin da Kotun Allah ya isa ta yanke, The Sun ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa a inuwa LP da Datti Baba-Ahmed sun yi wannan taro ne mako biyu bayan shugaba Tinubu ya samu nasara a Kotun ƙoli.

Da yake nasa jawabin, abokin takarar Obi watau Datti, ya jaddada cewa Kotu ba ta tabbatar da nasarar Tinubu ba amma ta goyi bayan ƙetare dokar da Kotun zaɓe ta yi.

A cewarsa, Kotun daga ke sai Allah ya isa ta amince da take dokar da Kotun sauraron kararrakin zaɓen shugaban ƙasa ta yi, amma ba ta tabbatar da nasarar Tinubu ba.

Kara karanta wannan

Peter Obi ya caccaki hukuncin Kotun Ƙoli kan nasarar Tinubu, Ya faɗi illar da ta yi wa ƴan Najeriya

Datti ya ce mutumin da ya yi jabun satifiket dinsa kuma yake da kashin kaji a safarar miyagun ƙwayoyi ba zai taɓa girgiza shi ba.

A kalamansa, ya ce:

"Kotun koli ba ta tabbatar da shugabancin Bola Ahmed Tinubu, ta dai tabbatar da take dokar ƙaramar Kotu."

INEC ta bi umarnin Kotun ɗaukaka ƙara

A wani rahoton na daban Hukumar zabe ta ƙasa INEC ta yi gyara a jerin sunayen ƴan takarar da zasu fafata a zaben gwamnan jihar Bayelsa.

A sabon jerin sunayen da INEC ta buga a shafinta, ta ƙara sunan ɗan takarar APC, Timipre Sylva da mataimakinsa, Maciver Joshua.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262