Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar Sanata Abba Moro Na Jam'iyyar PDP

Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar Sanata Abba Moro Na Jam'iyyar PDP

  • Kotun sauraron ƙararrakin zaɓen ƴan majalisar tarayya a jihar Benue ta tabbatar da nasarar Sanata Abba Moro na jam'iyyar PDP
  • Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan takarar jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Mista Daniel Onjeh ya shigar
  • Mai shari'a Ory Zik-Ikeorha ta yi hukunci cewa mai shigar da ƙarar ya kasa kawo gamsassun hujjoji kan ƙarar da ya shigar

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Benue - Kotun sauraron ƙararrakin zaɓen ƴan majalisar tarayya a jihar Benue ta tabbatar da nasarar sanatan Benue ta Kudu, Sanata Abba Moro na jam'iyyar PDP.

Kotun mai alƙalai uku wacce mai shari'a Ory Zik-Ikeorha take jagoranta ta yi fatali da ƙarar da Mista Daniel Onjeh na jam'iyyar All Progressives Congress (APC), ya shigar yana ƙalubalantar nasarar Sanata Abba Moro.

Sanata Abba Moro ya yi nasara a kotu
Kotu ta tabbatar da nasarar Sanata Abba Moro Hoto: Comrade Abba Moro/Daniel Onjeh
Asali: Facebook

Idan za a iya tuna wa dai hukumar zaɓe ta bayyana Sanata Abba Moro a matsayin wanda ya lashe zaɓen sanatan Benue ta Kudu wanda aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

Kara karanta wannan

Dan Majalisar Jam'iyyar Labour Party Da Kotu Ta Kora Ya Yi Martani, Ya Bayyana Matakin Dauka Na Gaba

Rashin gamsuwa da hakan ya sanya Mista Onjeh ya shigar da ƙara a kotun inda ya yi zargin cewa Sanata Moro bai lashe zaɓen da yawan ƙuri'u ba, sannan ba a gudanar da zaɓen bisa tanadin sabuwar dokar zaɓe ba.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kotu ta zartar da hukuncinta

Da take yanke hukunci kan ƙarar a ranar Lahadi, 10 ga watan Satumba a birnin Makurdi, mai shari'a Zik-Ikeorha, ta yi hukunci cewa shaidun da mai shigar da ƙarar ya kawo sun yi kaɗan su tabbatar da zargen-zargen da yake yi.

Mai shari'ar ta kuma yi nuni da cewa shaidun da masu shigar da ƙarar suka gabatar sun yi rauni sosai.

Mai shari'ar ta yi watsi da ƙarar sannan ta tabbatar da nasarar Sanata Abba Moro a matsayin sanatan Benue ta Kudu, rahoton Daily Post ya tabbatar.

Kara karanta wannan

Kotun Zabe Ta Tabbatar Da Nasarar Dan Majalisar APC a Jihar Benue

Lauyoyi sun yi martani kan hukuncin kotun

Da yake martani kan hukuncin kotun, lauyen Onjeh, Mista Tunde Oso, ya bayyana cewa zai tattauna da wanda yake karewa kafin yanke shawarar matakin da za su ɗauka na gaba.

A na sa ɓangaren, lauyan Moro, Mista Rafael Adakole ya bayyana cewa kotun ta tabbatar da zaɓin da mafi yawan al'ummar Benue ta Kudu suka yi ne ta hanyar yin adalci a shari'ar.

Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar Dan Majalisar APC

A wani labarin na daban, kotun zaɓe ta tabbatar da nasarar ɗan majalisar APC mai wakiltar Ado/Okpokwu/Ogbadibo, Philip Agbese.

Kotun ta yi fatali da ƙarar da abokan takararsa suka shigar suna ƙalubalantar nasarar da ya samu a zaɓen ranar 25 ga watan Fabrairu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng