Bala Muhammad Ya Aike da Sunayen Kwamishinoni 24 Ga Majalisar Dokokin Bauchi

Bala Muhammad Ya Aike da Sunayen Kwamishinoni 24 Ga Majalisar Dokokin Bauchi

  • Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad, ya nada kwamishinoni 24 kuma ya aika sunayensu zuwa majalisar dokokin jihar
  • Kakakin majalisa, Abubakar Y. Suleiman, ya karanto jerin sunayen kwamishinonin da gwamnan ya aiko a zaman ranar Litinin
  • Majalisar za ta tantance wadanda aka mika mata sunayensu a tsakanin 2, 3 da 4 ga watan Agusta mai kamawa

Bauchi - Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya aike wa majasar dokokin jihar da sunayen mutanen da yake son nada wa kwamishinoni.

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa gwamnan ya tura sunayen mutane 24 ga majalisar dokokin Bauchi domin tantance su da kuma tabbatar da su a matsayin kwamishinoni.

Gwamnan Bauchi ya tura sunayen wadanda yake so a nada kwamishinoni zuwa majalisa
Bala Muhammad Ya Aike da Sunayen Kwamishinoni 24 Ga Majalisar Dokokin Bauchi Hoto: Nigerian Tribune
Asali: UGC

Kakakin majalisar, Abubakar Y. Suleiman, ne ya karanta sakon mai girma gwamna a zaman majalisar na ranar Litinin, 24 ga watan Yuli.

Kara karanta wannan

Majalisa Ta Amince Abba Gida-Gida Ya Naɗa Wani Shehin Malami da Mace a Matsayin Kwamishinoni

Da yake karanto wasikar, ya ce sun samu sako daga gwamna inda ya nemi su tantance da tabbatar da nadin mutanen a matsayin kwamishinoni kuma mambobin majalisar zartarwa na jihar daidai da tanadin kundin tsarin mulki na 199.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jerin sunayen kwamishinonin

Shugaban masu rinjaye a majalisar, Saleh Hodi Jibir, ya karanto sunayen wadanda aka nada kamar haka:

  1. Maiwada Bello
  2. Ibrahim Gambo (Alkaleri)
  3. Mahmoud Babamaji Abubakar
  4. Danlami Ahmed Kawule (Bauchi)
  5. Tsammani Lydia Haruna (Bogoro)
  6. Ahmed Sarki Jalam (Dambam)
  7. Yakubu Ibrahim Hamza (Darazo)
  8. Usman Santuraki (Dass)
  9. Abdul Hassan Gamawa
  10. Muhammad Salees (Gamawa)
  11. Dr Yakubu Adamu (Giade)
  12. Usman Abdulkadir Moddibo (Jama’are)
  13. Hajara Jibrin Gidado (Itas/Gadau)
  14. Farouk Mustapha (Katagum)
  15. Hajara Yakubu Wanka (Kirfi)
  16. Aminu Hammayo (Misau)
  17. Hassan El-Yakub (Ningi)
  18. Muhammad Hamisu Shira (Shira)
  19. Simon Madugu Yalams
  20. Abubakar Abdulhamid Bununu (Tafawa Balewa)
  21. amila Muhammad Dahiru
  22. Adamu Umar Sambo (Toro)
  23. Abdulrazak Nuhu Zaki
  24. Amina Muhammad Katagum (Warji)

Kara karanta wannan

Gwamna da Kan Shi Ya Jawo Jama'a Zuwa Sallar Ruwa Saboda Yankewar Damina

Yaushe za a tantance kwamishinonin da aka nada?

Majalisar ta yanke shawarar tantance wadanda aka nada a ranakun 2,3 da 4 ga watan Agustan 2023, rahoton Nigerian Tribune.

Jam'iyyar PDP na zargin APC da hannu a harin da aka kaiwa Atiku a Adamawa

A wani labari na daban, mun ji cewa jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta zargi jam'iyyar All Progressives Congress (APC) da alhakin kitsa harin da aka kaiwa dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Atiku Abubakar.

A ranar Lahadi, 23 ga watan Yuli, wasu da ake zaton yan Boko Haram ne suka farmaki tsohon mataimakin shugaban kasar a gidansa da ke garin Yola, babban birnin jihar Adamawa kuma mahaifarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng