Shehu Sani Ya Shawarci Tinubu Da Kar Ya Aikata Kurakurai Guda 2 a Gwamnatinsa

Shehu Sani Ya Shawarci Tinubu Da Kar Ya Aikata Kurakurai Guda 2 a Gwamnatinsa

  • Sanata Shehu Sani ya shawarci Tinubu ya kiyayi aikata manyan kurakurai biyu a gwamnatinsa
  • Shehu Sani ya ba Tinubu shawarar ya kiyayi bai wa ministocin Buhari kariya, da kuma bai wa tsoffin gwamnoni mukamai
  • Shawarar ta Shehu Sani na zuwa ne a daidai lokacin da 'yan Najeriya ke jiran fitowar ministocin Tinubu

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani ya shawarci Shugaba Bola Tinubu da ya kiyayi aikata manyan kurakurai guda biyu a gwamnatinsa.

Shehu ya bayyana hakan ne a shafinsa na sabuwar kafar sada zumuntar nan ta Threads ranar Asabar.

Shehu Sani ya shawarci Tinubu kan abubuwa guda 2
Shehu Sani ya shawarci Tinubu kan bai wa ministocin Buhari kariya. Hoto: Shehu Sani, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

'Yan Najeriya na jiran Tinubu ya saki sunayen ministocinsa

Shawarar ta Shehu Sani na zuwa ne a daidai lokacin da 'yan Najeriya ke ci gaba da zaman jiran fitowar sunayen mutanen da Shugaba Tinubu zai naɗa a matsayin waɗanda da za su yi aiki tare da shi.

Kara karanta wannan

Tinubu Ya Yi Abin da Ya Gagari Buhari, Ya Sasanta Rikicin Hukumomi 2 a Cikin Wata 1

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Mutane sun yi ta hasashen waɗanda suke tunanin Shugaba Tinubu zai naɗa a matsayin ministoci a gwamnatinsa.

A cikin 'yan kwanakin nan ne aka ji Dele Alake ya fito yana nesanta fadar shugaban ƙasa da wasu sunaye da aka riƙa yaɗa cewa na ministocin ne.

Dele Alake, wanda shi ne mai magana da yawun Shugaba Tinubu, ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Alhamis kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Abubuwa 2 da Shehu Sani ya faɗawa Tinubu ya kaucemawa a gwamnatinsa

1. Shehu Sani ya ce yana da kyau Tinubu ya guji ba da kariya ga tsofaffin ministocin da suka yi aiki a ƙarƙashin gwamnatin Buhari yayin da aka zo gudanar da bincike a kansu.

2. Sannan Shehu Sani ya kuma bai wa Tinubu shawara kan cewa ya kar ya bai wa tsofaffin gwamnonin da aka tabbatar da sun kwashe dukiyar jihohinsu muƙami a gwamnatinsa.

Kara karanta wannan

Asalin Abin da Ya Kai Ni Wajen Tinubu a Aso Rock – ‘Dan Takaran Shugaban Kasa a PDP

An nemi Tinubu ya hana Ganduje muƙami ya bai wa Rarara

Legit.ng a baya ta kawo muku rahoto kan wani ɗan jam'iyyar APC a Kano da ya nemi Shugaba Bola Tinubu ya hana Ganduje muƙami, ya bai wa Rarara a maimakon haka.

Ya ce gudummawar da Rarara ya bai wa APC, ta fi wacce Ganduje ya bai wa jam'iyyar a lokacin zaɓe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng