Bidiyon Dala Na Ganduje Ya Zubda Kimar Kano a Idon Duniya, Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Kano

Bidiyon Dala Na Ganduje Ya Zubda Kimar Kano a Idon Duniya, Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Kano

  • Hukumar Karbar Korafe-Korafe Da Yaki Da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), ta ce bidiyoyin dala na Ganduje sun taɓa martabar Kano a idon duniya
  • Shugaban hukumar, Muhuyi Magaji Rimingado ne ya bayyana hakan yayin wani taro ranar Laraba a Kano
  • Muhuyi ya sha alwashin gudanar da bincike kan fayafayen bidiyon domin dawo da ƙimar jihar Kano a idon duniya

Kano - Hukumar karɓar korafe-korafe Da Yaki Da Rashawa ta jihar Kano (PCACC), ta ce bidiyon dala na tsohon gwamna Abdullahi Ganduje ya lalata martabar jihar a idon duniya.

Shugaban hukumar, Muhuyi Magaji Rimingado ne ya bayyana hakan, a wani taron wayar da kai kan yaƙi da cin hanci da rashawa kamar yadda Daily Trust ta wallafa.

Bidiyon dala ya zubar da kimar jihar Kano, in ji PCACC
Muhuyi Magaji ya ce bidiyon dala na Ganduje ya zubar da kimar Kano a idon duniya. Hoto: Barr. Muhuyi Magaji Rimingado
Asali: Facebook

Bidiyon dalar na Ganduje ya ɓata sunan Kano a wurare da dama

Kara karanta wannan

Bidiyon Dala: 'Binciken Kimiyya Ya Tona Wa Ganduje Asiri,' Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Kano

Ya ce rahotanni da dama na nuni da cewa bidiyon dalar na Ganduje, ya jawowa Kano zagi a wurare da dama har zuwa ƙasashen ƙetare.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Muhuyi ya ce a dalilin hakan ne ya sha alwashin ganin ya binciki bidiyon domin dawo da ƙimar jihar Kano a idon duniya.

Ya ƙara da cewa tun lokacin da aka fitar da bidiyon, mutane sun ƙalubalanci hukumar da ta tabbatar da ta binciki tsohon gwamnan don tabbatar da laifinsa ko akasin haka.

Sai dai ya ce hakan bai yi wu ba saboda rigar kariyar da Ganduje yake da ita a lokacin.

Da yaushe aka fitar da bidiyon Ganduje na karɓar Dala?

A shekarar 2018, jaridar Daily Nigerian ta fitar da wasu fayafayen bidiyo na Ganduje da aka yi zargin yana karɓar cin hanci daga hannun ‘yan kwangila.

Kara karanta wannan

Ganduje Ya Shiga Tasku a Yayin Da Hukumar Yaki Da Cin Hanci Ta Sake Fara Bincike Kan Bidiyonsa Na Daloli

A cikin faifan bidiyon, an hangi Ganduje na tattara kan dalolin, sannan kuma ya zurara su cikin aljihun babbar rigarsa.

Sai dai Ganduje ya musanta zargin, yana mai cewa fayafayen bidiyon duk na bogi ne.

Binciken ƙwaƙwaf ya bayyana gaskiya kan bindiyon dala na Ganduje

Legit.ng ta kawo muku wani rahoto da Hukumar karɓar korafe-korafe da yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta fitar dangane da bidiyon dala na Ganduje.

Hukumar ta ce binciken ƙwaƙwaf da aka gudanar a kan bidiyon, ya bayyana cewa bidiyoyin ba na bogi ba ne.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng