Ranar Da Shugaba Tinubu Zai Iya Mika Sunayen Ministocinsa a Gaban Majalisa Ta Bayyana

Ranar Da Shugaba Tinubu Zai Iya Mika Sunayen Ministocinsa a Gaban Majalisa Ta Bayyana

  • Gwamnonin da ke kan mulki, tsaffin gwamnoni da jiga-jigan ƴan jam'iyyu na ta ƙoƙarin miƙa sunayen ministoci ga Shugaba Tinubu
  • Mambobin jam'iyyar New Nigeria People's Party (NNPP) da Peoples Democratic Party (PDP) na faɗi tashin ganin sun shiga cikin jerin ministocin
  • Majiyoyi sun bayyana cewa ana saran Tinubu zai miƙa sunayen ministoci ga majalisar dattawa lokacin da ta dawo zamanta a ranar 4 ga watan Yuli

FCT, Abuja - Wani sabon rahoto ya nuna cewa akwai yiwuwar Shugaba Bola Tinubu ya tura sunayen ministocinsa ga majalisar dattawa bayan ranar 4 ga watan Yulin 2023.

A satin da ya gabata, majalisar dattawa ta ɗage zamanta har zuwa ranar Talata, 4 ga watan Yuli, cewar rahoton The Guardian.

Shugaba Tinubu zai aike da sunayen ministocinsa ga majalisa
Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Hoto: @DOlusegun
Asali: Facebook

Rigima yayin da shugabannin APC ke kokowar samun gurabe a jerin ministoci

Kara karanta wannan

Rikicin Cikin Gida Yana Neman Ya Kaure a APC a Kan Kujerun Ministocin Tinubu

A lokacin da majalisar za ta ci gaba da zamanta, ana saran Shugaba Tinubu ya kammala haɗa sunayen ministocinsa domin miƙa wa a gaban majalisar ta tantancesu.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Ƴan siyasa na ci gaba da faɗi tashi domin ganin sun samu gurabe a cikin ministocin Shugaba Tinubu. Gwamnoni da ke kan mulki, tsaffin gwamnoni da jiga-jigan jam'iyyar All Progressives Congress (APC) na ta kokawar ganin sun samu gurabe a cikin ministocin.

A cewar rahoton Vanguard, kamun ƙafar bai tsaya kawai a ƴan jam'yyar APC ba.

Jiga-jigan jam'iyyun adawa irinsu Peoples Democratic Party (PDP) da New Nigeria People's Party (NNPP) su ma suna da muradin samun gurabe a cikin ministocin.

Amma shugabannin APC basu goyon bayan hakan. Daga cikin ƙorafin da jiga-jigan na APC su ke kawo wa shi ne halastattun ƴan jam'iyyar APC kawai yakamata a zaɓa a matsayin ministocin.

Kara karanta wannan

Gwara Haka: Dakarun Sojin Sama Sun Soye Kwamandojin ISWAP a Wani Hari Kan Maboyarsu a Jihar Borno

Muhimman Wuraren Da Shugaba Tinubu Ya Kawo Sauyi

A wani labarin na daban kuma, kun ji cewa tun bayan rantsar da shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya kawo sauye-sauye a wurare da dama a ƙasar nan.

Fannin tattalin arziƙi na daga cikin wuraren da sabon shugaban ƙasar ya fara durfafa domin kawo sauyi a cikinsa, saboda rawar da yake takawa wajen ci gaban ƙasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng