Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Katsina da Taraba
Ɗan takarar gwamnan APC, Dikko Radda ya kaɗa kuri'a
Mai neman zama gwamnan jihar Katsina a inuwar jam'iyar APC, Dakta Dikko Umaru Raɗɗa, ya kaɗa kuri'arsa.

Source: Facebook
Dan takarar gwamnan PDP ya kaɗa kuri'a
Ɗan takarar gwamnan jihar Katsina karkashin inuwar PDP, Sanata Garba Yakubu Lado Ɗanmarke, ya kaɗa kuri'arsa a mazaɓarsa da ke Ɗanmarke, karamar hukumar Kankara.

Source: Facebook
Matar Radda Ta Jefa Kuri'a
Hajiya Fatima Dikko Ummaru Raɗɗa, matar ɗan takarar gwamnan jihar Katsina a inuwar jam'iyyar APC mai mulki ta ƙaɗa kuri'a.

Source: Facebook
Tsohon gwamna, Barista Shema ya kaɗa kuri'a
Tsohon gwamnan jihar Katsina na tsawon zango biyu, Barista Ibrahim Shehu Shema, ya kaɗa kuri'arsa a mzabarsa da ke yankin ƙaramar hukumar Dutsin-ma jihar Katsina.

Source: Facebook
Rumafar zabe mai mutum 13 kacal a Dabai
Malaman zaɓe na wucin gadi na zaune suna jiran mutane 13 kacal da suka yi rijistar zaɓe a PU 022 da ke gundumar Dabai, ƙaramar hukumar Ɗanja.
Yayin da wakilin Legit.ng Hausa ya ziyarci rumfar zaben, ya samu bayanin cewa mutane 7 sun samu damar kaɗa kuri'a, saura mutum 6 ake jira.

Source: Original
Shugaba Muhammadu Buhari ya kaɗa kuri'a
Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya kaɗa kuri'arsa a zaben gwamna da mambobin majalisar dokoki da ke gudana yau Asabar 18 ga watan Maris, 2023 a Katsina.
Buhari ya jefa kuri'rasa a mazabarsa da ke Daura kamar yadda, Bashir Ahmad, mai taimakawa shugaban kasa kan harkokin kafafen sada zumunta na zamani ya wallafa.
Zabe ya kankama a Dabai Ward, Danja LGA
Zabe ya kankama a PU OO1 da ke makarantar Model Firamare Dabai, ƙaramar hukimar Ɗanja a jihar Katsina.
Wakilimmu ya ziyarcu wurin kuma ya tarad da mutane a kan layi suna jira a tantance su kana su kaɗa kuri'unsu ga yan takarar da suka kwanta masu a rai.

Source: Original
An fara kaɗa kuri'a a Mashi LG
Tuni Malaman zaɓe suka gama shiri kuma har mutane sun fara kaɗa kuri'unsu a rumfar zabe ta 005 da ke makarantar Firamarea Gamzo, ƙaramar hukumar Mashi, jihar Katsina.

Source: Facebook