Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja

Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja

A yau Asabar, 18 ga watan Maris ne ake gudan da zaben gwamnoni da yan majalisar jihohi a fadin jihohi 28 cikin 36 na Najeriya.

Yan Najeriya za su sake komawa rumfunar zabe domin zabar wadanda suke so su jagorance su a matakin jiha na tsawon shekaru hudu masu zuwa.

A wannan zauren Legit.ng Hausa za ta kawo maku yadda zaben ke gudana a jihohin Sokoto da Neja.

Zaben gwamnan Neja

A jihar Neja za a fafata tsakanin yan takara 15 ne a zaben gwamnan na yau Asabar, sai dai ana ganin zaben zai fi zafi ne tsakanin jam'iyyar APC mai mulkin jihar, PDP, NNPP, LP da kuma APGA masu hamayya.

Yan takarar gwamna a jihar Neja
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: BBC Hausa
Asali: UGC

Muhammad Umar Bago shine dan takarar jam’iyyar APC a jihar Neja yayin da Isah Liman Kantigi ke rike da tutar PDP a jihar

Har ila yau a zaben gwamnan na Neja akwai kuma Yahaya Yahaya Sokodeke na NNPP. Jushua Bawa na LP da Khadija Iya Abdullahi a APGA da sauransu.

Zaben gwamnan Sokoto

Zaben gwamnan jihar Sokoto zai kasance daya daga cikin zabuka da za su dauki hankali sosai a fadin kasar kuma za a fafata ne tsakanin yan takara daban daban.

Yan takarar gwamna a jihar Sokoto
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: BBC Hausa
Asali: UGC

A yan takarar gwamnan jihar Sokoto, akwai Ahmad Aliyu Sokoto wanda ke rike da tutar jam'iyyar APC yayin da Sa'idu Umar ke rike da tutar PDP, Umar Dahiru Tambuwal na NNPP.

Sauran sune Ibrahim Muhammad Liman, dan takarar jam'iyyar ADP, Abubakar Umar Gada na jam'iyyar SDP da Aminu Umar Ahmad na Labour.

Janar Abdulsalami Abubakar ya kada kuri’arsa

Tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Janar Abdulsalami Abubakar, ya kada kuri’arsa a garin Minna, babban birnin jihar Neja.

Tsohon shugaban kasa Abdulsalam yana kada kuri'arsa
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: @TheNationNews
Asali: Twitter

Dan takarar gwamnan PDP a Sokoto ya nuna karfin gwiwar shi zai yi nasara

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Sokoto, Mallam Saidu Umar, ya kada kuri’arsa a rumfar zabe ta 020 Ubandoma, Sabon-titi, Kofar Atiku ta Sokoto.

Da yake jawabi ga manema labarai jim kadan bayan ya kada kuri'arsa, Mallam Umar ya ce zuwa yanzu zaben na gudana cikin kwanciyar hankali da lumana yankunan jihar.

Ya ce zaben yau ya fi na shugaban kasa da aka yi yan makonni da suka gabata inda ya nuna karfin gwiwar cewa shine zai yi nasara a zaben, rahoton Thisday.

Dan takarar gwamnan PDP a Sokoto yana kada kuri'arsa
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: @THISDAYLIVE
Asali: Twitter

Dan takarar gwamnan APC a Neja ya kada kuri'arsa

Dan takarar gwamnan APC a jihar Neja, Muhammad Umar Bago ya isa mazabarsa inda ya kada kuri’arsa a zaben gwamna da na majalisar jiha da ke gudana.

Dan takarar gwamnan APC a Neja yana kada kuri'arsa
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: @HonBago
Asali: Twitter

Yadda guragu suka yi tururuwan fitowa zabe a Minna

Yayin da zaben gwamna ke ci gaba da gudana a jihar Neja, kungiyar masu lalurar nakasa sun ce ba za a barsu a baya ba.

An dai ga guragu da dama a wata rumfar zabe da ke garin Minna inda suka fito don sauke hakkinsu na yan kasa.

Guragu a wajen kada kuri'a a garin Minna
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: @vanguardngrnews
Asali: Twitter

Tsohon gwamnan Neja ya kada kuri’arsa

Tsohon gwamnan jihar Neja, Muazu Babangida Aliyu, ya kada kuri’arsa a rumfar zabensa da ke unguwar Tunga a Minna, babban birnin jihar.

Babangida Aliyu yana kada kuri'arsa
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: @TheNationNews
Asali: Twitter

Rikici ya barke a wata rumfar zabe Karamar Hukumar Sokoto ta Arewa

An samu hatsaniya bayan wasu matasa sun hana jama’a yin zabe a wata rumfa da ke unguwar Dandima, Karamar Hukumar Sokoto ta Arewa.

Zabe a karamar hukumar Kontogora ta jihar Neja

Da misalin karfe 9:50, zabe na gudana a rumfar sakandare ta gwamnati a karamar hukumar Kontagora ta jihar Neja.

Hakazalika na’urar BVAS na tafiya daidaiba tare da kowani tangarda ba.

Yadda wakilin PDP a rumfar zabe ya kada kuri’a a madadin masu zabe a Sokoto

A rumfar zabe ta 008, Gidan Yumfa, jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke karamar hukumar Wamakko ta jihar Sokoto, an gano wakilin PDP a rumfar yana kada kuri’a a madadin masu zabe, kamar yadda Sahara Reporters ta rahoto.

Wakilin PDP yana kada kuri'a a madadin masu zabe
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: @SaharaReporters
Asali: Twitter

An fara kada kuri’a a rumfar zabe ta Bakin-Iku a jihar Neja

A yanzu haka, jama’a sun fara kada kuri’a a rumfar zabe ta Bakin-Iku da ke Karamar Hukumar Tafa, a Jihar Neja kamar yadda jaridar Aminiya ta kawo.

Jama'a na kada kuri'arsu a rumfar zabe
Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamna Ke Gudana a Jihohin Sokoto Da Neja Hoto: @aminiyatrust
Asali: Twitter

Ana shirin fara zabe a rumfar zabe ta Lambar Tukera, karamar hukumar Sokoto

Da misalin karfe 8:33 na safe, jami’an INEC sun kammala duk wani tsare-tsare a gudunmar Tureka da ke karamar hukumar Sokoto.

Komai ya kammala tsaf a rumfar zabe ta Lambar Tukera inda ake shirin fara kada kuri’u.

An fara tantance masu zabe a karamar hukumar Sokoto ta kudu

Jama'a sun fara tururuwa zuwa rumfar zabensu a karamar hukumar Sokoto ta kudu.

Tuni jami'an hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) suka fara tantance masu kada kuri'a a yankin bayan masu zaben sun yi dogon layi.

Online view pixel