Kai Tsaye: Bayanai Kan Yadda Kamfen Tinubu/Shettima Ke Gudana Yau A Maiduguri

Kai Tsaye: Bayanai Kan Yadda Kamfen Tinubu/Shettima Ke Gudana Yau A Maiduguri

Birnin Maiduguri ta cika ta banbatse yayinda jirgin yakin neman zaben shugaban kasa na jam'iyyar APC babban birnin na jihar Borno.

Maiduguri itace mahaifar dan takarar kujerar mataimakin shugaban kasa, Kashin Shettima.

Jawabin Tinubu a taron

Dan takarar shugaban kasa na APC< Bola Ahmed Tinubu, ya gabatar da jawabinsa a filin kamfen.

Tinubu ya yi alkawarin farfado da tattalin arzikin Najeriya.

Yace:

"Mungode Borno kun yi mana hallaci. Zamu farfado da tattalin arziki, zamu kawo cigaba Najeriya."
"Wadanda suka san Legas, zasu iya banbanta tsakanin abinda muka samu a 1999."
"Gwamnatinmu ta al'umma ce, zamu kula da dukkanku. Farin cikinku ya zo, cigaba ya zo, and ina tabbatar muku cewa gwamnatinmu ta al'umma ce, don al'umma zatayi kuma al'umma zata zabe ta."
"Dukkanku na bukatar ingantaccen ilimi. Ilimi shine makami mafi girma saboda 'yayanku zasu amfana rana gobe."
"Ina fatan ranar Asabar, 25 ga Febriaru, 2023 zaku yi zabe."

Wasu sun sauya sheka daga jam'iyyun adawa zuwa APC

Shugaban uwar jam'iyyar ya karbi wasu sabbin masu sauya sheka zuwa jam'iyyar APC.

Sun hada da dan takarar kujerar Mataimakin gwamnan jihar karkashin jam'iyyar NNPP, dan takarar kujerar majalisar wakilai na NNPP, Muhammad Habib Kashim da Shugaban jam'iyyar PDP na karamar hukumar Kaga, Bilai Ali.

Hakazalika akwai Sakataren shirye-shirye na PDP, dan takarar majalisar Bayo, da kuma da Marte, Jidda Aji.

Jawabin Shugaban Uwar Jam'iyyar APC, Abdullahi Adamu

Shugaban Uwar Jam'iyyar APC, Abdullahi Adamu, ya bayyana cewa Allah ya riga ya baiwa jam'iyyar APC nasara a zaben 2023.

Abdullahi Adamu yace:

"Zamu ci zaben nan. Idan Allah ya yarda Asabar mai zuwa muna jiran rantsuwa ne kawai."

Jawabin Shettima

Dan takarar mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya gabatar da jawabinsa ga al'ummar jihar Borno.

Shettima dai ya mulki jihar Borno tsawon shekaru takwas matsayin gwamnan jihar.

Ya fara jawabi da Hausa sannan kuma ya juya Kanuri.

A karamin jawabin da yayi da Hausa, ya bayyana cewa:

Ba abinda zan ce illa Allah ya saka da alheri
Insha Allah zamu rike amana.
Zamu karfafa batun samun mai a tafkin Chadi.

Yadda Tinubu ya shiga filin kamfe

Jama'a sun tarbi Bola Ahmed Tinubu tare da Kashim Shettima a cikin birnin Maiduguri.

Masoya APC na zaman jiran Tinubu

Daruruwan masoya jam'iyyar APC sun isa filin taron suna jira zuwan dan takarar shugaban kasa APC, Bola Ahmaed Tinubu.

Tinubu dai tun daren jiya ya dira Maiduguri don halartan kamfen.'

Birni
Kai Tsaye: Bayanai Kan Yadda Kamfen Tinubu/Shettima Ke Gudana Yau A Maiduguri
Asali: Twitter

Birni
Kai Tsaye: Bayanai Kan Yadda Kamfen Tinubu/Shettima Ke Gudana Yau A Maiduguri Hoto: @TheNationNews
Asali: Twitter

Borno
Kai Tsaye: Bayanai Kan Yadda Kamfen Tinubu/Shettima Ke Gudana Yau A Maiduguri Hoto: @TheNationNews
Asali: Twitter

Authors:
AbdulRahman Rashida avatar

AbdulRahman Rashida