Borno: ‘Yan Sanda Sun Gurfanar da Mutum 9 Kan Zargin Kaiwa Tawagar Atiku Farmaki

Borno: ‘Yan Sanda Sun Gurfanar da Mutum 9 Kan Zargin Kaiwa Tawagar Atiku Farmaki

  • Abdul Umar, kwamishinan ‘yan sanda na jihar Borno, ya tabbatar da kama wasu matasa kan zarginsu da ake yi da kaiwa tawagar Atiku Abubakar farmaki
  • Kwamishinan ‘yan sandan ya sanar da cewa 12 daga cikinsu duk magoya bayan jam’iyyar APC ne yayin da 2 daga ciki ne kacal ‘yan PDP
  • Ya yabawa Gwamna Zulum kan umarnin da ya bayar na kamawa tare da gurfanar da duk wani wanda ya tada tarzoma yayin siyasa a fadin jihar

Borno - Kwamishinan ‘yan sandan jihar Borno, Abdul Umar, yace rundunar ta gurfanar da mutum 9 da take zargi da kaiwa tawagar ‘dan takarar shugabancin kasa na PDP, Alhaji Atiku Abubakar, farmaki a jihar.

Kwamishinan ‘yan sanda
Borno: ‘Yan Sanda Sun Gurfanar da Mutum 9 Kan Zargin Kaiwa Tawagar Atiku Farmaki. Hoto daga dailytrust.com
Source: UGC

Kwamishinan ‘yan sandan wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a ranar Alhamis, yace jimillar mutum 14 masu tada tarzoma a yayin lamurran siyasa suka kama a jihar.

Kara karanta wannan

'Yan Bindiga Sun Kaiwa Ayarin Dakarun Yan Sanda Hari a Arewa, An Rasa Rayuka

Daga cikin mutum 14 da ake zargin, Umar yace 12 daga ciki magoya bayan jam’iyyar APC ne yayin da sauran 2 suka kasance magoya bayan jam’iyyar PDP.

“Duk da akwai zargin cewa wani ya mutu, har a halin yanzu ba a ga gawar ba.”

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

- Yace.

Yace an dauka matakai ba kadan ba daga wurin ‘yan sanda domin dakile dabanci a jihar, Daily Trust ta rahoto.

Ya yabawa gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum da ya basu umarnin gaggawa wurin kama duk wani mutum da yake kawo hayaniya yayin kamfen, komai matsayinsa, a kai shi kotu.

Kwamishinan ‘yan sandan yace rundunar ta kama mutum 119 da ake zargi sun tafka laifuka har da bata yaran mutane da shan miyagun kwayoyi.

Zuki ta Malle: APC tayi martani kan Kaiwa Atiku farmaki a Borno

A wani labari na daban, jam’iyyar APC mai mulkar jihar Borno ta musnata labarin da ake yadawa na cewa ‘yan jam’iyyar APC sun kaiwa Atiku Abubakar farmaki a jihar.

Kara karanta wannan

'Yan Sandan Sun Cika Hannu Da Manajan Cibiyar Zana Jarabawar JAMB, Bisa Zargin Salwantar Da Kwamfuwotoci 83

Kamar yadda Sanata Dino Melaye ya bayyana, miyagun ‘yan daba sun kaiwa tawagar ‘dan takarar shugabancin kasa na PDP, Atiku Abubakar, farmaki a jihar Borno.

Sai dai a martanin jam’iyyar APC, tace wannan tsabar karya ce da aka zabga amma babu wanda ya kai musu farmaki yayin kamfen din.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Khalid avatar

Aisha Khalid (Hausa editor) Aisha Khalid marubuciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018. Ta kwashe shekaru tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu. Za a iya tuntubar ta a adireshin email din ta kamar haka: aisha.khaleed@corp.legit.ng