Dan Takarar Shugaban Kasa, Al-Mustapha Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnan PDP Wike

Dan Takarar Shugaban Kasa, Al-Mustapha Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnan PDP Wike

  • Gwamnan PDP Wike na jihar Ribas ya karbi bakuncin dan takarar shugaban kasa a zabe mai zuwa a karkashin jam'iyyar Action Allience (AA)
  • Hamza Al-Mustapha ya dira gidan gwamna Wike, inda suka yi ganawar da ba a san me suka tattauna ba
  • Ana takun-saka tsakanin gwamnan Wike da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar

Jihar Ribas - Gwamnan Nyesom Wike na jihar Ribas ya yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar AA, Hamza Al-Mustapha a gidansa dake Fatakwal a daren ranar Litinin 12 ga watan Satumba.

Manjo Al-Mustapha (mai ritaya), wanda shi ne babban dogarin marigayi tsohon shugaban kasa, Sani Abacha ya kai wata ziyara ce a jihar ta Ribas.

Kara karanta wannan

Hotuna sun ba da mamaki yayin da Sarkin Musulmi ya gana da wani gwamnan Kudu

Gwamnan PDP ya mance Atiku, ya gana da dan takarar AA
Dan Takarar Shugaban Kasa, Al-Mustapha Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnan PDP Wike | Hoto: dailytrust.com
Source: UGC

Ziyarar ta Manjo na zuwa ne sama da mako guda bayan da masu neman kujerun gwamna 17 na jam’iyyar PDP a zaben 2023 suka zauna da Wike a Fatakwal.

Meye dalilin ganawar Wike da Al-Mustapha?

Ya zuwa yanzu dai ba a san dalilin wannan ganawa, kuma ba wannan karon farko da gwamnan ya karbi bakuncin wasu 'yan takara ba na jam'iyyarsa ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wata majiya daga gidan gwamnan Ribas ta shaidawa jaridar Punch cewa, gwamna Wike ko Al-mustapha babu wanda ya yiwa manema labarai bayanin me ya faru.

Sai dai, masu abin cewa na ganin ganawar na da alaka da neman goyon baya a zaben 2023 mai zuwa.

Haka nan, jaridar Daily Trust ta naqalto Al-Mustapha na cewa, ya kai ziyarar neman goyon baya ne ga gwamnan na PDP.

Tun bayan kammala zaben fidda gwanin shugaban kasa na PDP da kuma zabo gwamna Okowa a matsayin mataimakin Atiku, Wike ya karbi 'yan takara mabambanta a gidansa.

Kara karanta wannan

Yanzun nan: PDP ta fadi matsayar ta kan ko Ayu zai ci gaba da kasancewa shugabanta

Akwai takun-saka tsakanin dan takarar shugaban kasa na PDP Atiku Abubakar da kuma shi wannan gwamna na PDP.

Jam’iyyar PDP Ta Karbe Ofisoshin Yakin Neman Zaben Buhari Na Katsina

A wani labarin, jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa, reshenta a jihar Katsina ya karbe ofisoshin yakin neman zaben shugaban kasa Muhammadu Buhari a jihar.

Shugaban jam'iyyar ne na kasa, Iyorchia Ayu ya bayyana hakan ga manema labarai a jihar, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.

Ayu ya samu wakilicin hadiminsa a fannin yada labarai, Yusuf A. Dingyadi a jihar Katsina, inda yace tuni jijiyoyin PDP suka mamaye sassa daban-daban na mahaifar shugaban kasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng