Mun Shirya Zamu Fara Tallata Tinubu/Shettima Ga Yan Najeriya, Lalong

Mun Shirya Zamu Fara Tallata Tinubu/Shettima Ga Yan Najeriya, Lalong

  • Gwamna Jihar Filato, Simon Lalong, ya ce shiri ya yi nisa na fara yakin neman zaɓen Tinubu da Shettima a zaɓen 2023
  • Gwamnan wanda shi ne Darakta Janar na yaƙin neman zaɓen, ya gana da Bola Tinubu da kakakin majalisar wakilai a Abuja
  • Jam'iyyar APC ta naɗa gwamnan a matsayin Daraktan Kanfen ɗin ɗan takararta na shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu

Abuja - Jam'iyyar All Progressive Congress APC ta bayyana cewa shirye-shirye sun yi nisa na fara yaƙin neman zaɓen Tinubu/Shettimi a zaɓen shugaban kasa na 2023 da ke tafe, kamar yadda Punch ta ruwaito

Gwamnan Filato kuma Darakta Janar na yakin neman zaɓen ɗan takarar shugaban ƙasa na APC, Simon Lalong, shi ne ya yi wannan furucin bayan duba Hedkwatar Kanfen a Abuja.

Gwamna Simon Lalong na jihar Filato.
Mun Shirya Zamu Fara Tallata Tinubu/Shettima Ga Yan Najeriya, Lalong Hoto: The Plateau State Governor's Directorate Of Press/facebook
Asali: Facebook

Kakakin Gwamnan, Dakta Makut Macham, a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Jos, ya ce Sakataren Kanfen ɗin APC, Mista James Faleke, ne ya tarbi Lalong a Hedkwatar.

Kara karanta wannan

Shugaba Buhari Ya Sake Naɗa Tsohon Hadiminsa da Ya Yi Murabus, Ya Ba Shi Babban Matsayi

Hukumar Dillancin labarai ta ƙasa (NAN) ta rahoto Macham na cewa Daraktan Kamfen ɗin ya kuma gana da wasu mambobin tawagar yaƙin neman zaɓen a wani yunkuri na haɗa tawaga mai karfi don fuskantar kanfen.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Lalong Ya gana da Tinubu

Bayan haka, a rahoton jaridar Daily Trust, kakakin gwamnan ya ce:

"DG ya yi ganawar sirri da ɗan takarar shugaban ƙasa karkashin inuwar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, a Hedkwatar kamfen."
"Bayan haka kuma mutanen biyu sun shiga wani taron na daban da kakakin majalisar wakilai ta ƙasa, Femi Gbajabiamila da wasu yan majalisu daga majalisar dokokin jihohi."

A wani labarin kuma Gwamnan Adamawa zai jagoranci tawagar Atiku da zata sulhunta rikicin ɗan takarar da gwamna Wike

Ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya naɗa gwamnan Adamawa a matsayin shugaban tawagar sulhu da Wike.

Kara karanta wannan

Rikicin PDP: Atiku Ya Naɗa Gwamnan Arewa a Matsayin Shugaban Kwamitin da Zai Rarrashi Gwamna Wike

Ahmadu Fintiri, ya tabbatar da cewa kafin babban zaɓen 2023 komai zama tarihi a rikicin Atiku da gwamna Nyesom Wike.

Asali: Legit.ng

Online view pixel