Magana ta kare, watakila a tantance Gwamnan PDP a matsayin Abokin takarar Atiku a 2023

Magana ta kare, watakila a tantance Gwamnan PDP a matsayin Abokin takarar Atiku a 2023

  • Kwamitin Jam’iyyar PDP zai tantance wanda zai zama ‘dan takarar mataimakin shugaban kasa
  • Jam’iyyar PDP ta tsaida Alhamis ne a matsayin ranar da kwamitin da aka kafa zai yi wannan aiki
  • Debo Ologunagba ya ce Tom Ikimi ne zai yi wannan aiki tare da wasu kusoshin jam’iyyar adawar

Abuja - Jam’iyyar hamayya ta PDP ta kafa wani kwamiti na musamman da zai tantance mata ‘dan takarar kujerar mataimakin shuganan kasa a 2023.

Rahoto ya fito daga Daily Trust cewa Gwamna Nyesom Wike shi ne zabin da jam’iyyar ta yi. Sai dai har yanzu PDP ba ta fito an sanar da Duniya hakan ba.

A wani jawabi da sakataren yada labarai na PDP na kasa, Debo Ologunagba ya fitar, ya yi maganar tantance wanda zai tsaya takarar mataimakin shugaban kasa.

Kara karanta wannan

Kwamitin PDP sun zabawa Atiku wanda ya dace ya zama Mataimakinsa a zaben 2023

Mista Debo Ologunagba ya ce bangare na VI a sakin layi na 14 na dokar zaben jam’iyyar PDP ya yi bayanin kafa kwamitin da zai tantace ‘dan takaran na su.

Jawabin da Ologunagba ya fitar a ranar Talata ya nuna ‘yan majalisar NWC sun amince da wadanda za su zauna a kwamitin da zai yi aikin tantancewar.

Wannan kwamiti ne zai tantance ya kuma tabbatar da abokin takarar Atiku Abubakar a zaben 2023.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Gwamna Nyesom Wike
Nyesom Wike ya na nada sababbin kwamishinoni Hoto: @GovWike
Asali: Twitter

Su wanene 'yan kwamitin?

Kamar yadda ya shaidawa manema labarai, Kakakin na PDP ya ce Cif Tom Ikimi zai jagoranci aikin kwamitin a ranar Alhamis a sakatariyar jam’iyyar a Abuja.

Sauran ‘yan kwamitin sun hada da Kyaftin Idris Wada, Osita Chidoka, Rt. Hon. Binta Bello, Rt. Hon. Austin Opara, Farfesa Aisha Madawaki sai Fidelis Tapgun.

Kara karanta wannan

Arewa, da jerin kalubale 7 da suke jiran Peter Obi idan ya tsaya takarar Shugaban kasa

Atiku ya canza tsari a 2023

A wani rahoton, an ji shugaban PDP na kasa, Dr. Iyorchia Ayu yana umartar ‘yan jam’iyyar su karkare maganar ‘dan takara daga Laraba zuwa ranar Juma’a.

Iyorchia Ayu ya ce a wannan karo Atiku ya bukaci jam’iyya ta zaba masa wanda ya kamata ya zama abokin takararsa, akasin yadda ya yi lokacin zaben 2019.

Iwhnurohna Monitoring Group

Labarin da mu ka samu daga Premium Times ya nuna ‘yan kungiyar IMG ta mutanen Neja Delta da ke zama a Turai da Amurka su na goyon-bayan Nyesom Wike.

Kakakin kungiyar, Chindah Wami ya roki alfarma wajen Atiku Abubakar da ya zabi Wike ya zama masa mataimaki domin PDP ta kai ga nasara a zabe mai zuwa.

Dazu an ji labari cewa a karshe da aka je aka dawo, Kwamitin da Jam’iyyar PDP ta kafa ya zakulo babban abokin adawar Atiku Abubakar ne a zaben tsaida gwani.

Kara karanta wannan

Kusoshi a Jam’iyya sun dage Tinubu ya dauki Mataimaki daga mutum 2 a Gwamnatin Buhari

Majiyoyi sun tabbatar da cewa ‘Yan kwamitin na Janar Aliyu Gusau sun fi natsuwa da Gwamnan jihar Ribas a kan Gwamnonin jihohi ukun da aka yi la’akari da su.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng