Da dumi-dumi: An bindige mamban kwamitin zaben fidda gwanin APC a Taraba

Da dumi-dumi: An bindige mamban kwamitin zaben fidda gwanin APC a Taraba

  • Labarin dake shigowa daga Jalingo na nuna cewa an kaiwa daya daga cikin mambobin kwamitin asibiti hari
  • Shugaban kwamitin yace an bindige shi kuma an garzaya da shi gadon asibiti
  • Jihar Taraba kadai ta zabi tsarin yar tinke wajen zaben fidda gwanin yan takaran gwamnan APC

Jalingo - An bindige daya daga cikin mambobin kwamitin shirya zaben fiddan gwanin jam'iyyar All Progressives Congress APC a jihar Taraba.

Yanzu haka an garzaya da shi asibiti rai hannun Allah, rahoton ChanneltsTV.

Shugaban kwamitin, Lawrence Onuchukwu, ya laburtawa manema labarai a hedkwatar hukumar yan sandan jihar dake Jalingo, da daren Alhamis.

Da dumi-dumi: An bindige mamban kwamitin zaben fidda gwanin APC a Taraba
Da dumi-dumi: An bindige mamban kwamitin zaben fidda gwanin APC a Taraba
Asali: Original

An samu matsala: 'Yan bindiga sun harbe deliget 3 na zaben gwamnan PDP

A Neja kuwa, wasu ‘yan bindiga sun kashe deliget-deliget uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja, Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Da duminsa: EFCC ta gurfanar da Rochas Okorocha kan zargin damfarar N2.9bn

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban kwamitin zabe kuma mataimakin gwamnan jihar Bayelsa Lawrence Ewhrudjakpo ne ya sanar da haka a sakatariyar jam’iyyar PDP ta jihar, wurin da aka gudanar da zaben fidda gwanin.

An ce an kashe su ne a ranar Larabar da ta gabata yayin da suke komawa Mariga bayan da jam’iyyar ta dage zaben fidda gwanin sakamakon zanga-zangar da wasu ‘yan takara suka yi da nuna rashin amincewa da jerin sunayen wasu deliget din.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng