Abinda ya kamata ka sani game da mutum 23 ke son gadon Buhari karkashin APC

Abinda ya kamata ka sani game da mutum 23 ke son gadon Buhari karkashin APC

Bayan jeka-ka-dawo da yan siyasa suka yi na sayan Fom din takara karkashin jam'iyya mai ci ta All Progressives Congress (APC), mutum 23 kadai suka cike Fom din kuma suka mayar.

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Amma har yanzu ana tattaunawa shin wa jam'iyyar ta APC za ta baiwa tikitin takara kujerar shugaban kasa.

Shin me yasa mutane da yawa ke neman zama shugaban kasa? Wai me suke so ne? Shin kujerar shugaban kasa ta zama ta kowani irin mutu? Shin don son kasa sukeyi ko son kawunansu? Shine mutum nawa cikinsu zasu iya mulkar kasa irin Najeriya?

Amma yanzu an zo wajen, za'a tantance yan takara kuma saura kwanaki goma zaben tsayar da gwani.

Ga jerin mazaje 22 da mace daya dake neman kujerar shugaban kasa karkashin jam'iyyar APC:

1. Asiwaju Bola Ahmed Tinubu

Kara karanta wannan

Jerin gwamnonin APC da na PDP da basa neman zarcewa a 2023

Tsohon gwamnan jihar Legas (1999-2007)

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

2. Yahaya Adoza Bello

Gwamnan jihar Kogi (2016 - yanzu)

3. Dave Umahi

Gwamnan jihar Ebonyi (2015- yanzu)

4. Emeka Nwajiuba

Karamin Ministan Ilimi (2019 -2022)

5. Chibuike R. Amaechi

Kakakin majalisar dokokin jihar Rivers (1999-2007), Tsohon gwamnan jihar Rivers (2007-2015), Ministan Sufuri (2015-2022).

6. Fasto Nicholas Felix

Fasto mazauni kasar Amurka

7. Farfesa Yemi Osinbajo

Tsohon Fasto kuma Mataimakin shugaban kasa (2015- kawo yanzu)

8. Ken Nnamani

Tsohon Shugaban majalisar dattawan Najeriya

9. Fasto Tunde Bakare

Tsohon abokin takaran Shugaban Buhari a 2011 kuma Faston Latter Rain Assembly

10. OlaDimeji Bankole

Tsohon kakakin majalisar wakilan tarayya (2007-2011)

Abinda ya kamata ka sani game da mutum 23 ke son gadon Buhari karkashin APC
Abinda ya kamata ka sani game da mutum 23 ke son gadon Buhari karkashin APC
Asali: Facebook

11. Rochas Okorocha

Tsohon gwamnan jihar Imo (2011-2019), Sanata mai wakiltan Imo ta yamma (2019-yanzu)

12. Ibikunle Amosun

Tsohon gwamnan jihar Ogun (2011-2019),Sanata mai wakiltan Ogun ta tsakiya (2019-yanzu)

Kara karanta wannan

Jerin yan takarar shugaban ƙasa a APC da suka sayi Fom N100m kuma suka gaza maida wa

13. Sanata Robert Ajayi Boroffice

Sanata mai wakiltar Ondo ta Arewa (2011 - yanzu)

14. Ogbonnaya Onu

Ministan Kimiya da fasaha (2015 - 2022)

15. Benedict Ayade

Gwamnan jihar Cross Rivers (2015-yanzu)

16. Ahmad Ibrahim Lawan

Tsohon dan majalisan wakilai (1999–2007), Dan majalisan dattawa (2007-yanzu), Shugaban majalisar dattawa (2019-yanzu)

17. Ikeobasi Mokelu

Tsohon Ministan Labarai da al'adu lokacin gwamnatin mulkin soja n Janar Sani Abacha

18. John Kayode Fayemi

Gwamnan jihar Ekiti (2010-2014), Ministan ma'adinai (2015-2018), Gwamnan jihar Ekiti karo na biyu (2018-yanzu).

19. Mrs. Uju Kennedy

20. Abubakar Badaru Talamiz

Gwamnan jihar Jigawa (2015-yanzu)

21. Godswill Akpabio

Gwamnan jihar Akwa Ibom (2007-2015), Sanata (2015-2019), Ministan Neja Delta (2019-2022)

22. Ahmad Sani Yarima

Tsohon gwamnan jihar Zamfara (1999-2007), Sanata mai wakiltar Zamfara ta yamma (2007-2019)

23. Tein Jack-Rich

Shugaban kamfanin Belemaoil Producing Limited

Asali: Legit.ng

Online view pixel