Wasu Sun Rasa Abinci; Gwamna Inuwa Ya Rushe Majalisar Zartarwa
- Gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya raba mutanen da ke gwamnatinsa daga mukamansu bayan rushe majalisar zartarwa
- Muhammad Inuwa ya sanar da rushe majalisar zartarwar ne a ranar Laraba, 8 ga watan Afirilun 2026 yayin wani taro da aka gudanar
- Matakin gwamnan dai na zuwa ne yayin da aka fara shirya buga kugen siyasa domin tunkarar babban zaben shekarar 2027 da ake fuskanta
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Gombe - Gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya rushe majalisar zartarwa ta jihar.
Rushe majalisar zartarwar da Gwamna Inuwa Yahaya ya yi, ya nuna wani gagarumin sauyi a yanayin siyasar jihar.

Source: Facebook
Jaridar Daily Trust ta kawo rahoton cewa an bayyana hakan ne yayin taron majalisar zartarwa na jihar Gombe karo na 53, a ranar Laraba, 8 ga watan Afirilun 2026.
Gwamna Inuwa ya rushe majalisar zartarwa
Duk da cewa gwamnan bai bayyana dalilan rushe majalisar nan take ba, ana kyautata zaton matakin yana da alaƙa da wasu buƙatun siyasa da ke tasowa a tsakanin mambobin majalisar tasa.
Wannan matakin yana iya zama wani ɓangare na sauye-sauyen siyasa gabanin zaɓubbuka masu zuwa a jihar.
Ana sa ran Gwamna Inuwa Yahaya zai sake kafa wata sabuwar majalisa a kwanaki masu zuwa domin ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati da kuma dorewar shirye-shiryen da ake kai.
Ana sa ran samun ƙarin bayani kan wannan matakin da gwamnan ya dauka.
An fitar da sanarwa
Hakazalika, Shugaban sashen na yaɗa labarai na gidan gwamnatin Gombe, Ismaila Uba Misilli, ya sanar da rushe majalisar zartarwar a cikin wata takaitacciyar sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Laraba.
“Labari da dumi-duminsa.. Gwamna Inuwa Yahaya ya rushe majalisar zartarwa ta Gombe. “Ƙarin bayani na tafe.”
- Ismaila Uba Misilli

Source: Facebook
Ba a bayyana dalili ba
Bayanai game da dalilan rushe majalisar ba su fito fili ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Sai dai ana ran matakin zai shafi dukkan kwamishinoni da mambobin majalisar zartarwa na jihar dake kan mulki.
Ba a bayar da wani dalili na hukuma ba game da wannan shawara, amma masu sharhi na cewa irin waɗannan matakai galibi suna zama ɓangare na garambawul ga gwamnati ko kuma dabarun siyasa gabanin babban zaɓen 2027.
Karanta wasu labaran kan Gombe
- Dan majalisar PDP ya sauya sheka zuwa APC, ya hadu da Gwamnan Gombe
- Sheikh Pantami ya fadi dalilin shiga siyasa da neman gwamna a Gombe
- 'Yan Majalisa 2 sun fice daga jam'iyyar PDP, sun gana da shugaban gwamnonin Arewa
Gwamna Inuwa ya ba Daurawa gida
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kungiyar gwamnonin Arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya ba malamin addinin Musulunci, Sheikh Aminu Daurawa, gidan zama.
Gwamna Inuwa Yahaya ya ba Sheikh Aminu Daurawa gida a Gombe ne bayan shafe sama da shekara 20 yana zuwa jihar tafsirin Ramadan duk shekara.
Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana cewa 'yan kwanaki kafin shigar watan Ramadan shugaban gwamnonin Arewa, Inuwa Yahaya ya kira shi a waya cewa ya ba shi gida a Gombe.
Asali: Legit.ng


