An Yi Babban Rashi: Mataimakin Kwamishinan 'Yan Sanda a Najeriya Ya Rasu

An Yi Babban Rashi: Mataimakin Kwamishinan 'Yan Sanda a Najeriya Ya Rasu

  • Mutuwa mai yankar kauna ta ratsa rundunar 'yan sandan jihar Borno da ke yankin Arewa maso Gabas na tarayyar Najeriya
  • Mataimakin kwamishinan 'yan sandan jihar Borno da ke aiki a sashen binciken manyan laifuffuka, Abubakar Balteh, ya koma ga mahaliccinsa
  • Rundunar 'yan sandan jihar Borno ta tabbatar da rasuwar marigayin, inda ta bayyana musabbabin rasuwarsa a cikin wata sanarwa da ta fitar

​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Borno - Rundunar 'yan sandan jihar Borno ta yi rashi na daya daga cikin manyan jami'anta.

Mataimakin kwamishinan ’yan sanda (ACP) na sashen binciken manyan laifuffuka na rundunar, ACP Abubakar Balteh, ya riga mu gidan gaskiya.

Mataimakin kwamishinan 'yan sandan Borno ya rasu
Marigayi mataimakin kwamishinan 'yan sanda a Borno, Abubakar Balteh Hoto: Nahum Daso Kenneth
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a cikin wata gajeriyar sanarwa da jami'in hulda da jama'a na rundunar, ASP Nahum Daso, ya fitar a ranar Asabar, 21 ga watan Fabrairun 2026 a shafinsa na Facebook.

Kara karanta wannan

Kano: Sauya shekar Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jawo tarnaki a jam'iyyar APC

ASP Nahum Daso, ya bayyana cewa ACP Abubakar Balteh ya rasu ne a ranar 21 ga Fabrairu, 2026, sakamakon wani mummunan hatsarin mota.

"INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN"
"Rundunar ’yan sandan jihar Borno na baƙin cikin sanar da rasuwar ACP Abubakar A. Balteh, wanda ya riga mu gidan gaskiya a yau, 21 ga Fabrairu, 2026, sakamakon wani mummunan hatsarin mota."
"Har zuwa lokacin rasuwarsa, ya yi aiki cikin kwazo a matsayin mataimakin kwamishinan ’yan sanda na sashen binciken manyan laifuffuka (SCID) na rundunar jihar Borno."

ASP Nahum Daso ya bayyana cewa za a sanar da cikakkun bayanai game da shirye-shiryen jana’izarsa da sauran bayanan da suka shafi hakan nan gaba kadan.

"Za a sanar da cikakkun bayanai game da shirye-shiryen jana’izarsa da sauran bayanai masu alaƙa a lokacin da ya dace."
"Allah Madaukakin Sarki ya gafarta masa kurakuransa, Ya kuma ji kansa da rahama."

- ASP Nahum Daso

Idan za a iya tunawa, a watan Nuwamba na shekarar 2025, ASP Nahum Daso ya taba sanar da rasuwar mataimakin kwamishinan ’yan sanda (DCP) na sashen binciken manyan laifuffuka na rundunar, DCP Ahmed Ibn Umar, wanda ya rasu bayan ya yi fama da jinya.

Kara karanta wannan

Sojoji sun cafke mai kawo ga 'yan ta'adda, an kashe kwamandan Boko Haram

A waccan lokacin, jami’in hulda da jama’ar na rundunar 'yan sandan jihar Borno ya ce:

“Rundunar ’yan sandan jihar Borno na baƙin cikin sanar da rasuwar DCP Ahmed Ibn Umar, wanda ya rasu a asibitin koyarwa na jami’ar Maiduguri (UMTH) bayan ya yi fama da jinya.”
“Ya yi aiki cikin kwazo a matsayin mataimakin kwamishinan ’yan sanda na sashen binciken manyan laifuffuka (SCID) na rundunar jihar Borno. Allah ya jikansa da rahama.”

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng