Shugaba Tinubu Ya Fito Ya Nemi Afuwar 'Yan Najeriya bayan Fara Azumi

Shugaba Tinubu Ya Fito Ya Nemi Afuwar 'Yan Najeriya bayan Fara Azumi

  • Mai girma Bola Tinubu ya halarci bude Tafsirin Alkur'ani a fadar shugaban kasa ta Aso Rock Villa da ke birnin tarayya Abuja
  • Shugaba Tinubu ya yi jawabi a wajen Tafsirin, inda ya nuna muhimmancin da ke tattare da lokacin azumin watan Ramadan
  • Hakazalika, Shugaba Tinubu ya kuma mika kokon bararsa ga 'yan Najeriya kan su yi masa afuwa idan ya aikata ba daidai ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika kokon bararsa ga 'yan Najeriya yayin da aka fara azumin watan Ramadan.

Mai girma Shugaba Tinubu ya yi kira ga 'yan Najeriya da su yafe masa idan har ya yi musu laifi.

Shugaba Tinubu ya bukaci a yafe masa
Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Jaridar Daily Trust ta ce Shugaba Tinubu ya yi wannan roƙon ne ranar Laraba, 18 ga watan Fabrairun 2026 yayin buɗe Tafsirin Alkur'ani mai girma na wannan shekarar da aka gudanar a masallacin fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Kara karanta wannan

Bayan fara azumi, Shugaba Tinubu ya aika sako ga Musulmai da Kiristocin Najeriya

Tinubu ya yi magana kan azumi

Haka kuma, Tinubu ya yi magana kan haɗuwar watan azumin Ramadan da na Lent (azumin Kiristoci), inda ya ce hakan yana zama tunatarwa kan kyawawan ɗabi'u da dukkan addinan suka yi tarayya a kai.

“Azumin Ramadan ya zo daidai da na Lent, wanda hakan ke tunatar da mu kan kudurinmu guda na sadaukarwa, tarbiyya, addu’a, da kuma kame kai."
“Mun fara wannan Ramadan ne da dukkan koyarwar da yake ɗauke da ita gare mu baki ɗaya. Amma babban darasin shi ne kyautata wa mutane, yaɗa soyayya da imani, da kuma yafe wa juna. Ina cewa, idan na yi laifi, ku yafe mini a matsayinku na 'yan Najeriya.”

- Shugaba Bola Tinubu

Tinubu ya tunatar da 'yan Najeriya

Tinubu ya bayyana cewa ya kamata azumi ya wuce kawai barin ci da sha, ya ce dole ne ya zama alama ta nuna faffadar zuciya, yafiya, kyawawan ayyuka, da kuma son ɗan Adam, jaridar TheCable ta kawo labarin.

Kara karanta wannan

'Mulki mafi muni,' Hakeem Baba Ahmed ya yi gargadi kan tazarcen Tinubu a 2027

Ya bukaci 'yan Nijeriya na kowane addini da su yi addu'ar neman zaman lafiya tare da ba da goyon baya ga ƙoƙarin da ake yi na yaƙi da ta'addanci, 'yan bindiga, da sauran matsalolin tsaro.

Tun da farko a cikin sakonsa ga Kiristoci da Musulmai, Shugaba Tinubu ya buƙaci mabiya addinan da su kasance kankan da kai a cikin ayyukansu ga Allah.

Shugaba Tinubu ya ce haɗuwar waɗannan lokuta biyu a rana guda yana tunatar da mu cewa a matsayinmu na mutane masu addini, muna da abubuwa da dama da muka yi tarayya a kai, kuma mu al’umma ɗaya ne a wajen Allah.

Shugaba Tinubu ya jawo hankalin 'yan Najeriya
Mai girma Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Najeriya Hoto: Kashim Shettima
Source: Facebook

Babban limami ya yi nasiha

Shi ma a nasa jawabin, babban limamin masallacin fadar shugaban kasa, Abdulwahid Suleiman, ya gode wa Allah da ya nuna wa al'ummar Musulmi wani sabon lokacin azumi na Ramadan.

Ya yaba wa salon shugabancin Tinubu tare da yin addu'ar neman lafiya, da karfi ga shugaban da tawagarsa, sannan ya roƙi Allah ya tabbatar da zaman lafiya da ci gaba ga dukkan 'yan Najeriya.

Gwamna ya rage lokacin aiki saboda azumi

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya saukakawa ma'aikatan gwamnati saboda shigowar watan azumin Ramadan.

Kara karanta wannan

Basarake ya shiga har Aso Villa ya nemi Tinubu ya saki Nnamdi Kanu

Gwamna Nasir Idris ya amince da rage lokacin tashi daga wurin aiki domin ma'aikata su samu saukin gudanar da azumi.

A cikin sanarwar da aka fitar an bayyana cewa za a rika tashi daga wurin aiki da karfe 2:00 na rana a ranakun Litinin zuwa Alhamis.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng