'Yan Bindiga Sun Farmaki Kauyuka cikin Dare, An Yi Awon Gaba da Mutane a Katsina

'Yan Bindiga Sun Farmaki Kauyuka cikin Dare, An Yi Awon Gaba da Mutane a Katsina

  • 'Yan bindiga dauke da makamai sun kai hare-haren ta'addanci a wasu kauyukan karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina
  • Tsagerun 'yan bindigan sun yi awon gaba da mutane da dama a yayin hare-haren da suka kai cikin kauyukan da daddare
  • Majiyoyi sun bayyana cewa 'yan bindigan sun dauki lokacin suna barna tare da sanya jama'a cikin firgici yayin hare-haren da suka kai

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Katsina - ’Yan bindiga dauke da manyan makamai sun kai hare-hare kan wasu kauyuka a jihar Katsina.

'Yan bindigan sun sace mutane da dama a jerin hare-haren dare da suka gudana lokaci guda.

'Yan bindiga sun kai harin ta'addanci a Katsina
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Shaidun gani da ido sun tabbatar da kai harin ga tashar Channels Tv ta wayar tarho a ranar Talata, 6 ga watan Janairun 2025.

'Yan bindiga sun kai hare-hare a Katsina

Kara karanta wannan

Halin da masu zuwa Mauludi suke ciki bayan kwashe kwanaki hannun 'yan bindiga a Plateau

Sun bayyana cewa hare-haren sun faru ne a daren Litinin, 5 ga watan Janairun 2025 lokacin da ’yan bindigan da ke dauke da manyan makamai suka mamaye yankunan da abin ya shafa.

Tsagerun 'yan bindigan sun kwashe tsawon sa’o’i suna barna da tayar da hankulan jama'a a kauyukan da suka kai hare-haren, rahoton Daily Post ya tabbatar da hakan.

Majiyoyin tsaro sun ce ’yan ta’addan sun fara kai hari ne a Unguwar Alhaji Barau, daga nan suka wuce zuwa Gidan Dan Mai-gizo da kuma Gidan Hazo, dukkansu na cikin gundumar Na’alma a karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.

Me hukumomi suka ce kan lamarin?

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba, kuma har yanzu ba a tantance adadin mutanen da aka kashe ko aka sace ba.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ’yan sandan jihar Katsina, Abubakar Sadiq, ya bayya cewa bai samu labarin harin ba, amma ya yi alkawarin bincike tare da bayar da bayani.

“Don Allah bari na bincika, domin yanzu ne kawai nake jin labarin harin daga gare ku. Zan dawo da bayani."

Kara karanta wannan

Babbar magana: 'Yan bindiga sun kai kazamin hari 'wurin shakatawa' na gwamnatin tarayya

- Abubakar Sadiq

'Yan bindiga sun yi awon gaba da mutane a jihar Katsina
Taswirar jihar Katsina, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

'Yan bindiga na kai hare-hare a Katsina

Malumfashi na daga cikin kananan hukumomin Katsina da ke sahun gaba wajen fuskantar hare-haren ’yan bindiga, duk da yarjejeniyoyin zaman lafiya da aka shiga kwanan nan tsakanin shugabannin yankin da wasu kungiyoyin masu dauke da makamai.

Sababbin hare-haren sun zo ne bayan harin masallaci da ya faru a ranar 19 ga Agusta, 2025, inda ’yan bindiga suka kai farmaki wani masallaci, suka bude wuta kan masu ibada, suka kashe akalla mutane 32 a Unguwar Mantau, karamar hukumar Malumfashi.

Wata mazauniyar kauyen Danjanku a karamar hukumar Malumfashi ta bayyana cewa suna rayuwa cikin dar-dar.

Hussaina Kabir ta shaidawa Legit Hausa ayyukan da 'yan bindiga ke yi a yankinsu na sanya mutane cikin fargaba.

"Yan bindiga sun addabi yankinmu da hare-hare, muna rayuwa cikin fargaba saboda hare-haren da ake kawowa."
"Yakamata hukumomi su tashi tsaye domin kawo mana daukin da ya dace."

Kara karanta wannan

Nentawe: Shugaban APC ya kausasa harshe kan hare haren 'yan ta'adda a Neja

- Hussaina Kabir

Jami'an tsaro sun samu nasara kan 'yan bindiga

A wani labarin kuma, kun ji cewa jami'an tsaro sun samu nasara bayan sun gwabza fada da 'yan bindiga a jihar Zamfara.

Jami'an tsaron sun samu nasarar ceto mutane 20 da 'yan bindigan suka sace daga kauyen Dunfawa da ke yankin Moriki, a karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.

Aikin ceto mutanen ya samu nasara ne bayan hadin kai da tsare-tsaren jami’an tsaro da aka tura yankin, wanda ya tilasta wa ‘yan bindigan barin wadanda suka sace sannan suka tsere.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng