An Zo Wajen: Shugaban EFCC Ya Fallasa Hanyar da Gwamnoni Ke Sace Dukiyar Jama'a

An Zo Wajen: Shugaban EFCC Ya Fallasa Hanyar da Gwamnoni Ke Sace Dukiyar Jama'a

  • Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya koka kan yadda ake karkatar da kudaden jama'a
  • Ola Olukoyede wanda ya shiga ofis a 2023 ya yi zargin cewa wasu gwamnonin jihohi na sace kudaden tsaro da ake warewa duk wata
  • Shugaban na EFCC ya bayyana cewa matsalar cin hanci da rashawa ta zama musabbabin tabarbarewar rashin tsaro a kasar nan

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Legas - Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya yi zargi kan wasu gwamnoni.

Shugaban na EFCC ya zargi wasu gwamnonin jihohi da karkatar da biliyoyin Naira daga kudaden tsaro da ake warewa duk wata.

Shugaban EFCC ya yi zargi kan gwamnoni
Shugaban EFCC, Ola Olukoyede da tambarin hukumar Hoto: @OfficialEFCC
Source: Twitter

Shugaban EFCC ya yi zarge-zarge

Jaridar The Cable ta ce shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawar ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin wata lakcar shekara-shekara, a ranar Juma'a, 19 ga watan Disamban 2025.

Kara karanta wannan

Tura ta kai bango: Tinubu ya yi wa gwamnoni barazana kan kudin kananan hukumomi

An shirya lakcar ne a sansanin sojojin sama na Sam Ethnan, da ke a Ikeja, jihar Legas.

Ya ce sau da yawa ana mayar da kudaden zuwa kudin kasashen waje, sannan a ajiye su a kasashen waje maimakon a yi amfani da su wajen bunkasa tsaro.

Ola Olukoyede ya jaddada cewa cin hanci da rashawa shi ne babban musabbabin tabarbarewar tsaro a Najeriya.

Shugaban na hukumar EFCC ya ce kudaden da aka ware domin tsaro ko rage talauci, amma aka sace su, ana amfani da su ne wajen karfafa ’yan bindiga, masu tayar da kayar baya da masu tsattsauran ra’ayi.

Gwamnoni na karkatar da kudaden tsaro

Da yake yin misali da shari’ar da ake yi wa tsohon gwamnan jihar Anambra, Willie Obiano, Olukoyede ya ce EFCC ta gano yadda ake zargin an karkatar da sama da Naira biliyan 4 daga kudaden tsaro.

Shugaban EFCC ya zargi gwamnoni da sace kudaden tsaro
Shugaban EFCC, Ola Olukoyede na jawabi a wajen taro Hoto: @OfficialEFCC
Source: Facebook
"Gwamnonin jihohi na karɓar biliyoyin Naira duk wata a matsayin kudaden tsaro ba tare da bayyana yadda aka yi da su ba."

Kara karanta wannan

EFCC ta cafke bokaye da kudin kasashen waje na boge bayan damfarar 'yan Najeriya

“Wadannan kudade, maimakon a zuba su wajen inganta tsarin tsaro, sau da yawa suna karewa a wajen 'yan canji, inda ake mayar da su kudin waje a kai su kasashen waje, ko kuma a batar da su a wuraren da ba su da alaka da tsaro."
“Da ace an kashe wadannan kudade yadda ya dace, da yanayin tsaron Anambra da jihohin da ke makwabtaka da ita ya fi yadda yake a yau.”

- Ola Olukoyede

Jami'an EFCC sun kai samame gidan Malami

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC), sun kai samame wani gidan tsohon Antoni Janar kuma Ministan shari'a, Abubakar Malami.

Kafin rufe gidan da ke birnin Abuja, motoci da dama na EFCC tare da jami’ai ɗauke da makamai ne suka mamaye shi.

Matakin na EFCC dai na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tsananta bincike kan zarge-zargen da ake yi wa tsohon Ministan na shari'a a gwamnatin marigayi Muhammadu Buhari.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng