Ganduje na Fuskantar Barazanar Shari'a game da Yi Wa Hisbah Kishiya a Kano

Ganduje na Fuskantar Barazanar Shari'a game da Yi Wa Hisbah Kishiya a Kano

  • Shirin Abdullahi Ganduje na kafa sabuwar Hisbah mai zaman kanta ya bar baya da kura a Kano wanda ya fara tayar da hankali
  • Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce, yayin da wasu ’yan siyasa ke barazanar kai batun kotu saboda dakila matsaloli
  • Bangaren Dr. Ganduje ya ce tsarin ba zai haifar da fitina ba, yana cewa tsofaffin ma’aikatan Hisbah ne suka roƙi a taimaka musu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Yunkurin tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje na kirkirar sabuwar Hisbah mai zaman kanta ya haddasa muhawara a jihar.

Al'ummar jihar Kano da dama ciki har da ’yan siyasa na nuna damuwa da yiwuwar karuwar matsalolin tsaro da lalata zaman lafiya.

An taso Ganduje a gaba kan shirin hukumar Hisbah
Fom din sabuwar Hisbah a Kano da Abdullahi Umar Ganduje a gefe. Hoto: Alameen Muhammad Gama|Abdullahi Umar Ganduje.
Source: Facebook

Rahoton BBC Hausa ya ce masu adawa suna ganin sabuwar kungiyar za ta iya tada rikici saboda dokar Kano ta tanadi ikon rundunar Hisbah tilo ba mai zaman kanta ba.

Kara karanta wannan

'Ku yi likimo', Ganduje ya fadawa 'yan APC dabarar nasara a 2027

Hisbah: Kwamishinan Ganduje ya soke shi

Hakan na zuwa ne bayan tsohon Kwamishina a gwamnatin Ganduje ya caccake shi game da shirin kafa hukumar a Kano.

Injiniya Muazu Magaji ya ce matakin na iya jawo rikicin addini da rarrabuwar kai a jihar Kano da Arewa gaba ɗaya idan ba a mayar da hankali ba.

'Yan Najeriya sun yi martani inda wasu suka ce adawar siyasa ce ke haifar da irin wadannan zarge-zarge ga Ganduje.

Mutane na ci gaba da korafi kan shirin Ganduje na kafa hukumar Hisbah
Tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje. Hoto: Dr. Abdullahi Umar Ganduje.
Source: Facebook

Ana barazanar kai Ganduje kotu kan Hisbah

Wani babban dan siyasa a jihar Ibrahim Al-Amin Little ya ja kunnensa yana cewa kafa wata sabuwar Hisbah zai baiwa wasu dama su kirkiro nasu kungiyoyi, lamarin da zai rikita tsaro.

Ibrahim Little wanda ya taba neman takarar gwamna ya ce matsayinsa na dan uwansa, yana gargadin Ganduje ya janye wannan lamari, domin shirinsu shi ne su garzaya kotu a tantance ikon sa.

A cewarsa, Hisbah ta yanzu doka ce ta kirkira ta, kuma tana da hurumin kama masu laifi da mika su ga hukumomin tsaro.

Kara karanta wannan

Abba ya yi ta maza, ya murkushe yunkurin Ganduje na kafa sabuwar Hisbah a Kano

Ganduje ya musanta maganar tada rigima

Sai dai bangaren Ganduje ya musanta fargabar, yana cewa jama’a ba su fahimci cewa sabuwar kungiyar taimako ce ga tsofaffin Hisbah da aka rusa ba.

Tsohon kwamishinansa, Mohammed Garba ya bayyana cewa mutanen sun roki Ganduje su taimaka masu su cigaba da ayyukan addini da alheri ne, ba wai su kafa runduna ba.

Rahotanni sun bayyana cewa an fara raba fom da cike takardu, tare da taron kaddamarwa da ya jawo mutane daga kananan hukumomi 44 na jihar.

Dan ADC a Kano ya tattauna da Legit Hausa

Adnan Mukhtar TudunWada ya nuna goyon bayansa ga matakin kai lamarin kotu duba da matsalar tsaro da ake fama da shi.

Ya ce:

"Eh kwarai muna goyon bayan a tafi kotu a kokarin kafa wata Hisbah da muke da ita, domin a wannan lokaci da muke fama da tabarbarewar tsaro ba lokaci ba ne da za a zo ana raba kan abin da ya shafi tsaro."

Kara karanta wannan

Jami'in kwastam da ya yi fatali da cin hancin $50,000 ya samu karin girma

Hon. Adnan ya ce wannan shiri na Ganduje ba zai haifarwa Kano da mai ido ba, ya bukaci a yi hakuri da hukumar Hisbah da ake da shi yanzu.

Ya yabawa Alhaji Ibrahim Al-Amin Little bisa matakin da ya dauka na cewa zai kai kotu abu ne mai muhimmanci da nuna kishin jihar Kano.

Matasan Kano sun gargadi Ganduje kan kafa Hisbah

A baya, kun ji cewa kungiyoyin matasa a yankin Arewa da ke jihar Kano sun taso maganar neman kirkirar wata hukuma mai kama da Hisbah a gaba.

Matasan sun soki yunkurin kafa sabuwar hukumar da za ta dauki jami’an da aka sallama, suna cewa hakan barazana ne ga jihar da kuma zaman lafiya.

Kungiyoyin sun ce “Gwamna Abba Kabir Yusuf kadai ke da ikon gudanarwa”, kuma duk wata sabuwar Hisbah ba ta da halaccin doka.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.