Kwana Ya Kare: Babban Jigon APC a Najeriya, Farfesa Abdulgafar Ya Kwanta Dama

Kwana Ya Kare: Babban Jigon APC a Najeriya, Farfesa Abdulgafar Ya Kwanta Dama

  • Shugaban Majalisar Gudanarwa na jami'ar OAU, Farfesa Abdulgafar Siyan Oyeweso ya riga mu gidan gaskiya yau Talata a jihar Osun
  • Marigayin, wanda jigo ne a jam'iyyar APC ya rasu ne bayan fama da gajeruwar jinya, yana da shekaru 64 da haihuwa
  • Iyalansa sun sanar da cewa za a yi wa mamacin jana'iza kamar yadda addinin musulunci ya tanada bayan sallar La'asar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Osun, Nigeria - Najeriya ta yi babban rashi da fitaccen Farfesa a fannin ilimin tarihi, Farfesa Abdulgafar Siyan Oyeweso ya riga mu gidan gaskiya.

Farfesa Oyeweso, wanda babban jigo a jam'iyyar APC mai mulkin kasar nan ne, ya rasu bayan fama da gajeruwar rashin lafiya, yana da shekaru 64 a duniya.

Siyan Oyeweso
Fitaccen Farfesan ilimin tarihi kuma jigo a APC, Abdulgafar Siyan Oyeweso Hoto: Mallam Nurudeen Babatunde
Source: Facebook

Gwamnatin Osun ta tabbatar da rasuwar

Mai taimaka wa Gwamna Ademola Adeleke kan Harkokin Kafofin Sada Zumunta, Azeez Badmus, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, kamar yadda Tribune Nigeria ta kawo labarin.

Kara karanta wannan

PDP ta manta da adawa, ta koma neman taimako wajen Shugaba Tinubu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Badmus ya yi ta’aziyya ga iyalan mamacin tare da bayyana bakin cikinsa kan wannan rashi, wanda ya ce ya shafi gaba daya al'ummar jihar Osun da Najeriya baki daya.

Ya rubuta cewa:

“Allah Ya ji kanka, Farfesa Siyan Oyeweso, ɗan asalin garin Ede mai daraja, abin alfahari ga jihar Osun da Najeriya baki daya. Wannan rashi babba ne kwarai."

Iyalan Farfesa Oyeweso sun fitar da sanarwa

A wata sanarwa daban, ƙanin mamacin, Olawale Oyeweso, ya tabbatar da rasuwar fitaccen malamin jami’an wanda ya yi da jami'ar Obafemi Awolowo watau OAU.

Sanarwar ta bayyana cewa har zuwa lokacin rasuwarsa, marigayin shi ne Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Obafemi Awolowo da ke Ile-Ife.

“Cikin kunci da bakin ciki muke sanar da rasuwar uba kuma ɗan’uwan mu, Shugaban Majalisar Gudanarwa (Council) na Jami’ar Obafemi Awolowo da ke Ile-Ife, Farfesa Abdulgafar Siyan Oyeweso.
"Ya rasu a ranar Talata, 2 ga Disamba, 2025, yana da shekara 64, bayan gajeriyar rashin lafiya. Abdulgafar Siyan Oyeweso, kwararren Farfesan Tarihi, malami kuma jagoran tarbiyya, ya haskaka rayuwar dubban ɗalibai, abokan aiki, da abokan siyasa.”

Kara karanta wannan

"Na gaji haka nan" Gwamna ya mika takardar murabus, ya fice daga jam'iyyar PDP

Siyan Oyeweso
Shugaban majalisar gudanarwa na Jami'ar OAU, Farfesa Siyan Oyeweso Hoto: Mallam Nurudeen Babatunde
Source: Twitter

An sa lokacin jana'iaza a Ede

Olawale Oyeweso ya kara da cewa mamacin ya rasu ya bar mata, ’ya’ya da sauran ’yan uwa, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

A cewar iyalinsa, za a yi jana'izarsa a garinsa na Ede da misalin ƙarfe 4:00 na yammacin yai Talata, bayan sallar La’asar.

Sanarwar ta ƙara da addu’ar cewa:

“Allah Ya ji kansa da rahamarsa, Ya sa shi Aljannatul Firdaus, Ya ba iyalansa da masoyansa haƙurin jure wannan babban rashi.”

Tsohon shugaban APC a Osun ya rasu

A wani rahoton, kun ji cewa an tabbatar da rasuwar Sarkin Igbajo na 30 kuma tsohon shugaban APC reshen jihar Osun, Oba Adegboyega Famodun.

Iyalan gidan sarautar sun bayyana cewa Famodun ya mutu ne a ranar Jumma'a, 28 ga watan Nuwamba, 2025 bayan gajeruwar jinya.

An ruwaito cewa a lokacin mulkinsa, Oba Famodun yi aiki tukuru wajen haɗa kan al’ummar Igbajo, tare da inganta zaman lafiya, fahimtar juna da ci gaba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262