Gwamnatin Tinubu Ta Dakatar da Batun Karbar Harajin Shigo da Fetur na Kashi 15
- Hukumar NMDPRA ta ce an dakatar da aiwatar da harajin shigo da man fetur da dizal da aka tsara na kashi 15
- NMDPRA ta tabbatar da cewa akwai wadataccen man fetur da dizal a kasar nan domin biyan bukatar jama’a
- Ta gargadi dillalai da ’yan kasuwar mai da su guji boye mai ko kara farashi ba bisa ka’ida ba a fadin kasar nan
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
FCT, Abuja – Gwamnatin tarayya ta dakatar da aiwatar da tsarin karɓar harajin shigo da mai da dizal na kashi 15 wanda aka tsara a baya.
Wannan na zuwa ne bayan fitar da sanarwa daga hukumar NMDPRA a ranar Alhamis, wacce ta bayyana cewa an janye aiwatar da shirin.

Source: UGC
Punch ta wallafa cewa daraktan sashen hulda da jama’a na hukumar, George Ene-Ita ne ya sanya hannu a kan sanarwar da aka fitar.

Kara karanta wannan
Bayan gargadin Birtaniya, gwamnatin Tinubu ta fitar da sakamakon yaki da ta'addanci na 2025
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A baya, shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da shirin saka wannan haraji domin karfafa tattali, sai dai gwamnatin ta sauya matsaya bayan nazari kan tasirin hakan a kan farashin mai.
NMDPRA ta ce akwai mai a Najeriya
A cewar hukumar, Najeriya na da isasshen mai da dizal a yanzu domin biyan bukatar jama’a a dukkan bangarori na kasa, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar karin amfani da mai.
Sanarwar ta ce:
“Akwai wadatar man fetur, dizal da iskar gas a cikin gida wanda ake samu daga matatun cikin gida da kuma ta hanyar shigo da kaya daga waje, domin tabbatar da cewa dukkan wuraren ajiya da tashoshin sayar da mai suna da isasshen kaya.”
Hukumar ta kuma bayyana cewa tana ci gaba da lura da yanayin wadatar kayayyakin mai a fadin kasa, tare da daukar matakan da suka dace don hana tangarda ko tashin farashi marar dalili.
An gargadi masu boye mai a Najeriya
Hukumar NMDPRA ta yi kira ga ’yan kasuwa da masu rarraba mai da su guji boye kaya ko yin karin farashi ba bisa yanayin kasuwa ba.

Source: Getty Images
Rahoton Channes TV ya nuna cewa hukumar ta ce boye mai zai iya haifar da matsalolin karancin fetur a wasu yankuna.
Ta ce:
“NMDPRA na amfani da wannan dama wajen jan hankalin jama’a da masu kasuwanci da su guji boye kaya ko kuma kara farashin man fetur da dizal ba bisa ka’ida ba.”
NMDPRA ta jaddada cewa tana aiki kafada da kafada da duk masu ruwa da tsaki a bangaren makamashi domin tabbatar da cewa akwai wadataccen mai a duk fadin kasar.
Tinubu ya yi kira ga 'yan jaridan Najeriya
A wani labarin, kun ji cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga 'yan jarida su rika masa adalci wajen sukar manufofinsa.
Shugaban kasar ya bayyana haka ne yayin taron 'yan jarida karo na 21 da aka gudanar a birnin tarayya Abuja ranar Laraba.
Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa ta dauki wasu matakai masu tsauri domin habaka tattalin arziki kuma da sannu za a ci moriyarsu.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Asali: Legit.ng

