'Yan Sanda Sun Ayyana Neman Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa, Sowore Ruwa a Jallo

'Yan Sanda Sun Ayyana Neman Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa, Sowore Ruwa a Jallo

  • Rundunar yan sanda ta umarci dakarunta su kama dan gwagwarmaya, Omoyele Sowore a duk inda suka gan shi a jihar Legas
  • Kwamishinan yan sandan jihar, Olorundare Jimoh ya ce sun samu labarin shirin da Sowore ya yi na tayar da zaune tsaye da sunan zanga-zanga
  • Rahotanni sun nuna cewa yan kungiyar Take It Back Movement da Sowore ke jagoranta sun fito zanga-zanga amma yan sanda sun kore su

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos, Nigeria - Rundunar 'Yan Sandan Jihar Legas ta ayyana dan gwagwarmaya kuma tsohon dan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore a matsayin wanda take nema ruwa a jallo.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta ware kusan N5bn don wasu muhimman ayyuka

Yan sanda sun dauki wannan matakin ne bisa zarginsa da yunkurin ta da zaune tsaye da hargitsi da sunan zanga-zanga a jihar Legas.

Dan gwagwarmaya, Omoyele Sowore.
Hoton dan gwagwarmaya, Omoyele Sowore Hoto: @OmoyeleSowore
Source: Facebook

Daily Trust ta ruwaito cewa a kwanakin baya, kwamishinan ‘yan sandan Legas, Olorundare Jimoh, ya gargaɗi Sowore da ya guji shirya zanga-zanga lam rusau da gwamnatin jihar ta aiwatar a unguwar Oworonshoki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sowore, jagoran “Take It Back Movement”, ya yi barazanar gudanar da zanga-zanga a makonnin baya domin nuna adawa da rusa gidajen da gwamnati ta yi da sunan shirin sabunta birni.

'Yan sanda sun tarwatsa zanga-zanga

Duk da gargaɗin da rundunar ta yi, magoya bayan wannan kungiya sun fito a ranar Litinin, sun fara gudanar da zanga-zangar lumana.

Sai dai jami’an ‘yan sanda na sashin tarwatsa tarzoma da na Rundunar Task Force sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa masu zanga-zangar

Rahotanni sun bayyana cewa Sowore, mamallakin jaridar Sahara Reporters, bai halarci zanga-zangar ba, kamar yadda Leadership ta ruwaito.

Dalilin neman Sowore ruwa a jallo

Kara karanta wannan

Juyin mulki: Mutanen da sojoji suka kama a gidan tsohon gwamna na ta shan matsa

Bayan jami’an tsaro sun tarwatsa masu zanga-zangar, Kwamishinan ‘yan sandan, Jimoh, ya bayyana Sowore a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo, bisa zargin kokarin tada tarzoma da gangan.

“Ya shirya dukkan tsare-tsare don toshe hanya a kan gadar Third Mainland Bridge, wannan babban laifi ne mai tsanani.
"Abin da yake son yi shi ne jefa ga al’umma cikin kunci da wahala, musamman matafiya da ke amfani da hanyar. Ba za mu bari hakan ta faru ba.
"Mun kusa kama shi kuma duk inda ya shiga ya buya, za mu zakulo shi. Muna da bidiyo da ke nuna cewa ya sauka daga jirgi daga Abuja amma bai fito ba saboda tsoron kama shi.”

- CP Olorundare Jimoh.

Dakarun yan sanda.
Hoto jami'an yan sanda a bakin aiki a Najeriya Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

Tuni dai aka jibge jami’an tsaro a manyan wurare a Legas, musamman a kan Gadar Third Mainland Bridge, domin hana duk wata zanga-zanga da ka iya haifar da cunkoson ababen hawa ko hargitsi a gari.

Sowore ya soki barazanar Trump

A wani rahoton, kun ji cewa dan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore ya soki barazanar shugaban Amurka Donald Trump ta turo sojoji su yi yaki a Najeriya.

Kara karanta wannan

'Kamar Libya, Iraq,' Sowore ya fadi hadarin zuwan sojojin Amurka Najeriya

Tsohon dan takarar shugaban kasa, Omoyele ya gargadi ‘yan Najeriya da su yi hattara da barazanar shugaba Donald Trump domin babu alheri a ciki.

Sowore ya bayyana cewa kalaman Trump na iya burge wasu, amma tarihi ya tabbatar da cewa irin mamayar Amurka ba sa kawo mafita.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262