Yadda Tankar Mai ta Kife a Neja, Jama’a Sun Shiga Matsanancin Yanayi
- An samu hadarin tankar mai a jihar Neja, lamarin da ya dagawa mazauna yankin Lapai hankali a ranar Lahadi
- Rahoto ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu jami’ai a hukumomi daban-daban suna nan suna aikin tabbatar da tsaro
- Ana yawan samun hadurran manyan motoci a Najeriya, wannan na da nasaba da yaddaa titunan kasar ke lalacewa
Lapai, Jihar Neja - Wata tanka mai ɗauke da man fetur ta kife a kan hanyar Lambata-Lapai-Agaie da ke Jihar Neja, lamarin da ya haifar da tashin hankali a tsakanin mazauna yankin.
Binciken ya nuna cewa tankar, wanda ta tashi daga Legos zuwa Kano, ta kife ne da safiyar Lahadi a ƙauyen Takalafiya, da ke cikin karamar hukumar Lapai ta jihar Neja.

Kara karanta wannan
Fadar Vatican da kanta ta tsage gaskiya kan zargin kisan Kiristoci, ta yi gargadi
Wani mazaunin garin Lapai, Mallam Mahmud Abubakar, ya shaida wa Daily Trust ta wayar tarho cewa wurin da tankar ta kife na kusan kilomita biyu ne kacal daga tsakiyar garin Lapai.

Source: Twitter
Dalilin kifewar tankar mai a Neja
Ya bayyana cewa wurin da tankar ta kife yana daga cikin sassan titin da aka gyara kwanan nan a ƙarƙashin shirin gyaran tituna na kamfanin NNPCL, amma cikin ɗan kankanin lokaci titin ya fara lalacewa.
A cewar Mahmud:
“Wurin nan da tankar ta kife an gyara shi ba da jimawa ba a cikin aikin NNPCL, amma yanzu ya fara lalacewa, shi ne ya jawo wannan hatsari.”
A wata majiyar kuma, Mohammed Hassan Sonmaji, ya ce gaggawar da sashen kashe gobara na Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBUL) tare da jami’an NSCDC suka yi, ita ce ta taimaka wajen kauce wa mummunan bala’i.
A cewarsa:
“Da ba a samu taimakon nan da wuri ba, da hatsarin nan ya iya zama bala’i mai girma, domin tankar cike rake da mai.”
Jami’an tsaro sun kawo daukin gaggawa
Ya kara da cewa jami’an Ƙungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas (NUPENG) reshen Lapai, sun isa wurin don taimakawa wajen sarrafa yanayin da abin ya faru.
Ya ce:
“Jami’an NUPENG sun kawo taimako domin a kwashe man da ya zube da kuma hana yaduwar haɗari.”
Rahotanni sun ce an tattara man da ya zube cikin ganguna domin kauce wa asara da kuma kare muhalli daga barna.
Hukumar Neja ta yi magana kan hadarin
Da aka tuntubi Dr. Ibrahim Audu Hussaini, darektan yada labarai da harkokin musamman na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), ya tabbatar da cewa babu abin da ya kamata a tayar da hankali a kai.
A kalamansa:
“Babu abin da ya kamata a damu da shi, tankar bata tashi da wuta ba. Motocin kashe gobara na jami’ar IBB Lapai suna wurin suna jiran ko wani abu zai faru.”
Ya kara da cewa jami’an tsaro ma sun isa wurin don tabbatar da cewa ba a samu wata matsala ko lalata dukiya ba.
Lamarin ya jawo cunkoson ababen hawa na ɗan lokaci a kan hanyar, yayin da jami’an tsaro suka ci gaba da tsare wurin domin kare rayuka da dukiyoyi.
An shiga fargaba a Neja bayan da tankar mai ta kife a Lapai
Asali: Legit.ng

