Jonathan Ya Fadi Tsohon Ministan da Ya Kamata 'Yan Siyasa Su Yi Koyi da Shi

Jonathan Ya Fadi Tsohon Ministan da Ya Kamata 'Yan Siyasa Su Yi Koyi da Shi

  • Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya bayyana halayen kirki da tsohon ministan noma, Audu Ogbeh, yake da su
  • Goodluck Jonathan ya bayyana Audu Ogbeh a matsayin mutum mai yafiya wanda ba ya riko a zuciyarsa
  • Tsohon shugaban kasan ya nuna cewa yana da hali irin na marigayin wanda ya taba shugabantar jam'iyyar PDP

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Tsohon shugaban kasa, Dr. Goodluck Jonathan, ya bayyana cewa bai rike kowa a zuciyarsa kan abubuwan da aka taba yi masa a baya

Goodluck Jonathan ya jaddada cewa yafiya da sulhu suna da matukar muhimmanci a siyasa, haɗin kan kasa da ci gaba.

Jonathan ya yaba da halayen Audu Ogbeh
Hoton tsohon shugaban kasan Najeriya, Goodluck Jonathan Hoto: Goodluck Jonathan
Source: Facebook

Jaridar The Punch ta ce ya bayyana hakan ne a daren Laraba a Abuja yayin taron addu’ar tunawa da tsohon ministan noma, Cif Audu Ogbeh.

Kara karanta wannan

'Kirista ne amma ya cancanci Aljanna,' El Rufa'i ya yi wa Ogbeh addu'ar rahama

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jonathan ya fadi halayen Audu Ogbeh

A cewar sanarwar da mai magana da yawunsa, Ikechukwu Eze, ya fitar, Jonathan ya bayyana marigayi Ogbeh a matsayin mutum mai sauƙin kai kuma mai yafiya, wanda ba ya riko a zuciya, tamkar yadda shi ma yake ɗaukar rayuwa.

"Cif Ogbeh mutum ne wanda ba ya neman ramuwar gayya. Ya yi imani cewa abin da ya wuce ya wuce."
"A wannan fannin, yana kama da ni. Idan ka cutar da ni yau, zan yafe maka. Ban yin kiyayya da kowa. Na yi imani abin da ya wuce ya wuce."

- Goodluck Jonathan

Jonathan ya bayyana cewa alakarsa da marigayi Ogbeh ta fara ne tun lokacin da yake mataimakin gwamna, yayin da marigayin yake shugaban jam’iyyar PDP.

“Ban san Cif Ogbeh ba sai da na zama mataimakin gwamna, lokacin yana shugaban PDP. A lokacin, ana kallon mataimakan gwamna kamar ‘tayar ajiya’, amma ya ɗauke ni a matsayin aboki na kusa."

Kara karanta wannan

Wike ya sake ballo aiki, ya fadi manyan abubuwan da ya damu da su

"Duk lokacin da na je Abuja, sai na kai ziyara wajensa, kuma muna yin tattaunawa mai ma'ana. Mutum ne mai kirki da karamci sosai."

- Goodluck Jonathan.

Ya kara da cewa zumuncin da ke tsakaninsu ya ci gaba har bayan da ya zama shugaban kasa, rahoton jaridar Vanguard ya tabbatar da labarin.

“Duk lokacin da yake so ya ganni, yana zuwa, kuma wani lokaci muna iya yin sa’a guda muna tattauna batutuwan kasa."

- Goodluck Jonathan

Goodluck Jonathan ya ba 'yan siyasa shawara
Tsohon shugaban kasan Najeriya, Goodluck Jonathan Hoto: Goodluck Jonathan
Source: Facebook

Wace shawara Jonathan ya ba 'yan siyasa?

Jonathan ya yi kira ga ‘yan siyasar Najeriya da su yi koyi da dabi’un Ogbeh na saukin kai, yafiya da iya haɗa kan jama’a daga sassa daban-daban.

Tsohon shugaban kasan ya jaddada cewa irin waɗannan kyawawan dabi’u ne ginshikin ci gaban ƙasa.

PDP ta magantu kan takarar Jonathan

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta bayyana matsayarta kan takarar Goodluck Jonathan a zaben 2027.

Jam'iyyar PDP ta bayyana cewa Jonathan yana da 'yancin yin takarar shugaban kasa a babban zaben shekarar 2027.

Kara karanta wannan

Bugaje: Tsohon dan majalisa ya 'karyata' Obasanjo kan neman wa'adi na 3

Hakazalika, jam'iyyar ta ce dole Goodluck Jonathan ya bi dukkan matakan da dokar jam’iyya ta shimfida don neman takarar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng