Wike Ya Sake Ballo Aiki, Ya Fadi Manyan Abubuwan da Ya Damu da Su

Wike Ya Sake Ballo Aiki, Ya Fadi Manyan Abubuwan da Ya Damu da Su

  • Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya yi magana kan sukar da mutane ke yi masa
  • Nyesom Wike ya bayyana cewa ko kadan bai taba damuwa da abin da mutane suke fadi a kansa ba
  • Ministan ya bayyana cewa babban abin da ya fi maida hankali kan yin aikin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba shi

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana cewa ba zai taɓa bari batanci ko sukar jama’a su yi tasiri a kansa ba.

Wike ya jaddada cewa damuwarsa ita ce yadda zai farantawa Allah da kuma yin aikinsa kamar yadda Shugaba Bola Tinubu ya umurce shi.

Wike ya caccaki masu sukarsa
Hoton ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike Hoto: Nyesom Ezenwo Wike - CON, GSSRS
Source: Facebook

Jaridar Leadership ta ce Wike ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a wajen kaddamar da aikin gina hanyoyin unguwar Mabushi, Abuja, a ranar Litinin, 22 ga watan Satumban 2025.

Kara karanta wannan

Wike ya fadi abin da ƴan siyasar Ribas suka saka a gaba bayan dawowar Fubara

Nyesom Wike ya caccaki masu sukarsa

Wike ya yi kaca-kaca da masu sukarsa, yana zarginsu da kokarin amfani da batanci domin tilasta shi ya aikata abin da bai dace da ka’idarsa ba.

"To idan kuna so, ku tashi ku shirya kanku, kan wani abu da na sani ba daidai ba ne, idan kun ga dama ku yi kuka daga safe har dare, ku kira ni duk sunan da kuke so, ku saka sunana a intanet, ku faɗi duk abin da kuke so, babu matsala."

- Nyesom Wike

Wike ya jaddada cewa batanci wani abu ne da aka saba yakar 'yan siyasa da shi, amma bai isa ya sauya masa ra’ayi ba.

“Ni ba ni daga cikin waɗanda za ku yi tunanin batanci zai canja su. A matsayinka na ɗan siyasa, ya kamata ka sani cewa dole ne ka fuskanci irin waɗannan abubuwa, don me za ka damu?"

Kara karanta wannan

Wike ya tsallake rijiya, ya fadi yadda Janar na soja ya ba da umarnin harbe shi

"Babu wani ɗan siyasa da ya daɗe a siyasa da zai yi tunanin mutane ba za su fadi wani abu a kansa ba."

- Nyesom Wike

Wane abu ne ya damu Wike?

Ya kara da cewa abin da kawai zai iya damunsa shi ne idan Shugaba Tinubu ya nuna rashin gamsuwa da aikinsa, rahoton Daily Post ya tabbatar da labarin.

Wike ya yi magana kan masu sukarsa
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike Hoto: @GovWike
Source: Facebook
“Ranar da na shiga siyasa, na san cewa daga yanzu mutane za su fadi duk abin da suke so, don haka ku faɗa. Abin da kawai zai dame ni shi ne idan wanda ya naɗa ni bai gamsu da aikina ba."
"Amma saboda kawai ba mu yi abin da kuke so ba, sai ku yi zaton batanci zai tilasta mu yi, ba za mu yi ba."
"Ban taɓa cewa ina son na kasance cikin mutanen da ake so ba. A’a, ban son wani ya so ni. Abin da nake so kawai shi ne Allah."

- Nyesom Wike

Wike ya aika sako ga Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Kara karanta wannan

Shikenan: Za a rataye sojan Najeriya da ya hallaka mai 'Keke Napep' a Bauchi

Wike ya yabawa shugaban kasan ne kan matakin da ya dauka na janye dokar ta-bacin da ya sanya a jihar Rivers.

Ministan ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ya sake nuna jajircewarsa wajen tabbatar da dorewar dimokuradiyya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng