Takaddamar Akpabio da Natasha: Zanga Zanga Ta Barke a Majalisa, An Samu Bayanai

Takaddamar Akpabio da Natasha: Zanga Zanga Ta Barke a Majalisa, An Samu Bayanai

  • Magoya bayan Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan sun gudanar da zanga-zanga a harabar majalisar tarayya da ke birnin Abuja
  • Masu zanga-zangar waɗanda suka haɗa da mata da maza sun buƙaci shugaban majalisar, Godswill Akpabio ya bar muƙaminsa
  • Sun kuma buƙaci kwamitin ladabtarwa na majalisar dattawa da ya fasa binciken zargin rashin ɗa'a da ake yi wa Sanata Natasha
  • Jami'an ƴan sanda da ke majalisar a Abuja sun tarwatsa masu zanga-zangar ta hanyar harba musu hayaƙi mai sa hawaye

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Masu zanga-zanga da ke goyon bayan Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan sun mamaye ƙofar majalisar tarayya a ranar Laraba.

Masu zanga-zangar sun fito ne kan zargin cin zarafi da ake yi wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio.

Zanga zanga ta barke a majalisar tarayya
Magoya bayan Natasha sun yi zanga-zanga a Abuja Hoto: Natasha H. Akpoti, The Nigerian Senate
Asali: Twitter

Jaridar The Nation ta ce masu zanga-zangar, da suka haɗa da mata da maza daga yankin mazaɓar Kogi ta Tsakiya, suna ƙarƙashin jagorancin ɗaya daga cikin lauyoyin Sanata Natasha, Victor Giwa.

Kara karanta wannan

Natasha: 'Yan sanda sun tarwatsa masu zanga zanga, sun harba barkonon tsohuwa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me masu zanga-zangar suke so a yi?

Masu zanga-zangar sun riƙe kwalaye, tutoci, da alluna waɗanda suke ɗauke da saƙonni daban-daban.

Sun buƙaci kwamitin ladabtarwa da karɓar ƙorafe-ƙorafe na majalisar dattawa, wanda aka turawa binciken zargin rashin ɗa'ar Sanata Natasha da ya janye daga bincikarta.

A cewarsu, ba zai yiwu mutum ya zama alƙalin da zai yanke hukunci a kansa ba.

Sun buƙaci Sanata Godswill Akpabio da ya sauka daga muƙaminsa domin ba da dama a gudanar da binciken ba tare da nuna son zuciya ba.

Da yake jawabi yayin zanga-zangar, Victor Giwa ya bayyana cewa ofishin lauyoyinsu ya samu umarnin kotu da ke dakatar da kwamitin ladabtarwa na majalisar dattawa daga ci gaba da binciken.

Ya ce ba za a iya sa ran cewa shugaban kwamitin da mambobinsa za su yanke hukunci cikin adalci ba, kasancewar Akpabio ne ya naɗa su.

Ƴan sanda sun kori masu zanga-zanga

Kara karanta wannan

Zargin 'neman lalata' ya ƙara girma, Sanata Natasha ta gabatar da takarda a Majalisa

Jaridar TheCable ta rahoto cewa jami’an ƴan sanda sun fatattaki masu zanga-zangar.

Ƴan sandan sun harba hayaƙi mai sa hawaye domin hana magoya bayan Natasha Akpoti-Uduaghan shiga cikin harabar majalisar tarayyar.

Masu zanga-zangar dai sun fito ne da misalin ƙarfe 8:00 na safe kafin a fara zaman majalisar na ranar Laraba.

Sai dai, jami’an tsaron ba su yi wata-wata ba suka ci gaba da tarwatsa masu zanga-zangar ta hanyar harba musu hayaki mai sa hawaye.

Daga nan ne sai dandazon masu zanga-zangar su ka koma dandalin Unity Fountain.

Mutanen da Natasha ta zarga da ci mata zarafi

A wani labarin kuma, mun kawo muku manyan mutanen da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta taɓa zarga da ci mata zarafi.

Na baya-bayan nan daga cikinsu shi ne shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Godswill Akpabio wanda ya fito daga jihar Akwa Ibom.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng