Takaddamar Akpabio da Natasha: Zanga Zanga Ta Barke a Majalisa, An Samu Bayanai
- Magoya bayan Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan sun gudanar da zanga-zanga a harabar majalisar tarayya da ke birnin Abuja
- Masu zanga-zangar waɗanda suka haɗa da mata da maza sun buƙaci shugaban majalisar, Godswill Akpabio ya bar muƙaminsa
- Sun kuma buƙaci kwamitin ladabtarwa na majalisar dattawa da ya fasa binciken zargin rashin ɗa'a da ake yi wa Sanata Natasha
- Jami'an ƴan sanda da ke majalisar a Abuja sun tarwatsa masu zanga-zangar ta hanyar harba musu hayaƙi mai sa hawaye
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Masu zanga-zanga da ke goyon bayan Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan sun mamaye ƙofar majalisar tarayya a ranar Laraba.
Masu zanga-zangar sun fito ne kan zargin cin zarafi da ake yi wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio.

Asali: Twitter
Jaridar The Nation ta ce masu zanga-zangar, da suka haɗa da mata da maza daga yankin mazaɓar Kogi ta Tsakiya, suna ƙarƙashin jagorancin ɗaya daga cikin lauyoyin Sanata Natasha, Victor Giwa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Me masu zanga-zangar suke so a yi?
Masu zanga-zangar sun riƙe kwalaye, tutoci, da alluna waɗanda suke ɗauke da saƙonni daban-daban.
Sun buƙaci kwamitin ladabtarwa da karɓar ƙorafe-ƙorafe na majalisar dattawa, wanda aka turawa binciken zargin rashin ɗa'ar Sanata Natasha da ya janye daga bincikarta.
A cewarsu, ba zai yiwu mutum ya zama alƙalin da zai yanke hukunci a kansa ba.
Sun buƙaci Sanata Godswill Akpabio da ya sauka daga muƙaminsa domin ba da dama a gudanar da binciken ba tare da nuna son zuciya ba.
Da yake jawabi yayin zanga-zangar, Victor Giwa ya bayyana cewa ofishin lauyoyinsu ya samu umarnin kotu da ke dakatar da kwamitin ladabtarwa na majalisar dattawa daga ci gaba da binciken.
Ya ce ba za a iya sa ran cewa shugaban kwamitin da mambobinsa za su yanke hukunci cikin adalci ba, kasancewar Akpabio ne ya naɗa su.
Ƴan sanda sun kori masu zanga-zanga

Kara karanta wannan
Zargin 'neman lalata' ya ƙara girma, Sanata Natasha ta gabatar da takarda a Majalisa
Jaridar TheCable ta rahoto cewa jami’an ƴan sanda sun fatattaki masu zanga-zangar.
Ƴan sandan sun harba hayaƙi mai sa hawaye domin hana magoya bayan Natasha Akpoti-Uduaghan shiga cikin harabar majalisar tarayyar.
Masu zanga-zangar dai sun fito ne da misalin ƙarfe 8:00 na safe kafin a fara zaman majalisar na ranar Laraba.
Sai dai, jami’an tsaron ba su yi wata-wata ba suka ci gaba da tarwatsa masu zanga-zangar ta hanyar harba musu hayaki mai sa hawaye.
Daga nan ne sai dandazon masu zanga-zangar su ka koma dandalin Unity Fountain.
Mutanen da Natasha ta zarga da ci mata zarafi
A wani labarin kuma, mun kawo muku manyan mutanen da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta taɓa zarga da ci mata zarafi.
Na baya-bayan nan daga cikinsu shi ne shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Godswill Akpabio wanda ya fito daga jihar Akwa Ibom.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng