Bayan Rage Farashin Man Fetur, An Fara Maganar Karya Farashin Siminti a Najeriya
- Ministan ayyuka, Injiniya Dave Umahi ya bukaci masana'antun siminti su rage farashin kowane buhu ɗaya zuwa N7,000
- Umahi ya bayyana cewa Dala ta karye zuwa kusan N1,400, kuma an rage farashin fetur don haka ya kamata siminti ya sauka
- Ya gargaɗi masana'antun siminti cewa matukar ba su rage farashin kayansu ba, zai kai batun gaban Bola Ahmed Tinubu
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja - Ministan Ayyuka, David Umahi, ya bukaci masana'antun siminti su rage farashin kowane buhu daga sama da N9,000 da ake sayarwa a yanzu zuwa N7,000.
Umahi ya bayyana cewa farfaɗowar darajar Naira a kasuwar musaya da saukar farashin man fetur, dalilai ne masu ƙarfi da ya kamata su karya farashin siminti a Najeriya.

Asali: Twitter
Ministan ya danganta hakan da manufofin tattalin arziki da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bullo da su, wanda suka taimaka wajen ɗaga ƙimar Naira da rage farashin kayayyaki, rahoton The Nation.

Kara karanta wannan
A gaban Tinubu da manyan jiga jigai, Ganduje ya bankado abubuwan da ya tarar a APC
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Barazanar daukar mataki kan kamfanoni
A gefe guda, ministan ya gargadi kamfanin sadarwa na MTN da kamfanin gini na RCC Nigeria Ltd kan jinkirin da aka samu a aikin titin Enugu-Onitsha
A wata sanarwa da mai taimaka masa wajen yada labarai, Uchenna Orji, ya fitar, Umahi ya ce za su tuhumi MTN da alhakin duk wata matsalar kudi da za ta hana aikin ci gaba.
Ya kuma bayyana cewa gwamnati ba za ta amince da karin farashin aiki (VOP) ba har sai an kammala aikin.
Ministan ayyuka ya gana da MTN da RCC
Umahi ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi da wakilan MTN da RCC, wanda ƙaramin ministan ayyuka, Mohammad Bello Goronyo da babban sakataren ma’aikatar, O.O. Adebiyi suka halarta.
An tattauna batun kudin aikin titin Enugu-Onitsha da kuma wa’adin kammalawa, wanda aka sake tabbatar da ranar 10 ga Mayu, 2026.
Ministan ya jaddada cewa gwamnati ba za ta amince da wani karin kudi a aikin ba kuma RCC dole ne ta bi ka'idojin kwangila, ba wai yin aiki bisa ra'ayinta ba.
An buƙaci karya farashin siminti
Umahi ya ce:
"Ina farin ciki cewa manufofin shugaba Tinubu suna aiki. A yau, dala tana kusa da N1,400. A da, lokacin da dala ta kusan kai N2,000, farashin siminti ya tashi daga N7,500.
"To me ya sa yanzu da aka daidaita farashin canji, siminti har yanzu bai sauko daga N9,500 ba?"
Ya yi barazanar cewa idan masana'antun siminti ba su rage farashin zuwa N7,000 cikin mako guda ba, zai kai kara ga shugaba Tinubu don daukar mataki.

Asali: Facebook
Ɗangote ya rage farashin fetur
A wani labarin, kun ji cewa matatar hamshakin ɗan kasuwar nan, Alhaji Aliko Ɗangote ta rage farashin litar man fetur ana shirin fara azumin Ramadan.
A sanarwa da matatar Ɗangote ta fitar, ta bayyana cewa ta ruguzo da farashin kowace lita daga N890 zuwa N825.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng