Al'umma Sun Taso Sarki da Ya Yi Batan Dabo a Gaba Yayin da Matarsa Ke Sarauta

Al'umma Sun Taso Sarki da Ya Yi Batan Dabo a Gaba Yayin da Matarsa Ke Sarauta

  • Rashin sanin halin da Basarake Oba Joseph Olugbenga Oloyede a jihar Osun ya tayar da hankulan al'umma
  • Rahotanni sun tun Maris din 2024 babu duriyarsa inda al'ummar Ipetumodu ke neman bayanin inda yake
  • Wasu na zaton yana jinya a Amurka, amma wasu na kyautata zaton yana fuskantar shari'ar zamba kan kudin tallafin COVID-19
  • An bayyana cewa ya samu $4.2bn ta hanyar bogin kamfanoni, tare da wani mai suna Edward Oluwasanmi, wanda ake tuhuma a Amurka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Osogbo, Osun - An shafe watanni babu labarin Oba Joseph Olugbenga Oloyede, Apetu na Ipetumodu a jihar Osun.

Mazauna yankin sun roki Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, da ya binciki lamarin.

Ana zargin basarake da handame tallafin Covid-19 a Amurka
Al'umma a yankin jihar Osun sun bukaci sanin halin da sarkinsu ke ciki bayan watanni. Hoto: Legit.
Asali: Original

Al'umma sun bukaci bayani kan sarkinsu

Punch ta ce Oba Oloyede na zaune a Amurka, an nada shi sabon Apetu a watan Yulin 2019 bayan rasuwar Oba James Adegoke a 2017.

Kara karanta wannan

Canada ya yi martani kan rahoton hana hafsan tsaron Najeriya shiga kasarta

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun bayan nadinsa, ya kan rika tafiye-tafiye tsakanin Najeriya da Amurka, amma tun daga Maris 2024 da ya tafi bai dawo ba.

Wasu daga cikin mazauna garin sun ce suna jin yana jinya a Amurka, amma wasu na zaton yana fuskantar shari'ar damfara kan kudaden COVID-19.

Wani babban mutum a Ipetumodu ya bayyana cewa tun kusan shekara daya ba a ga Sarki a garin ba, kuma yana rasa tarukan al'umma.

A lokacin addu'ar Kiristocin Ipetumodu, an ga wanda aka ce shi ne Oba Oloyede a hoton bidiyo, amma fuskarsa ba ta bayyana sosai ba.

Oba Oloyede ya yi alkawarin dawowa kafin ƙarshen watan Janairun 2025 amma yanzu Fabrairu ta zo ba a gan shi ba.

Ana zargin ya rusa tsohon fadar sarauta kuma ya yi alkawarin gina sabuwa, amma har yanzu ba a ga sabon ginin ba.

Zargin da ake yi wa basaraken a Amurka

Rahotanni sun nuna cewa bai halarci bukukuwan gargajiya guda uku na garin ba, wanda hakan ya jawo rudani a tsakanin jama'a.

Kara karanta wannan

Yadda Kwankwaso ya fara gana wa da manyan 'yan siyasa gabanin zaben 2027

Wata majiya ta ce matar Sarki ce ke gudanar da harkokin mulki a madadinsa, lamarin da ke sa jama'a tambayar inda yake.

Rahotanni daga Amurka sun nuna cewa ana tuhumarsa da damfara kan kudaden tallafin COVID-19 na dala miliyan 4.2 tare da wani mai suna Oluwasanmi.

A wata hirar bidiyo, Oba Oloyede ya karyata jita-jitan cewa yana fuskantar shari'a, yana mai cewa maganganun makiya ne kawai.

Bayan nada sabon Sarki, rigima ta balle

Kun ji cewa sabuwar rigima ta barke a garin Esa-Oke da ke Osun bayan nadin Yarima Timileyin Oluyemi Ajayi a matsayin Olojudo na Ido Ayegunle.

Wasu da ba a san ko su wanene ba sun kai farmaki cikin garin, suka bude wuta kan jama’a, lamarin da ya jawo asarar rayuka.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

iiq_pixel