An Shiga Fargaba da Aka Kama Tulin Makamai Ana Yunƙurin Shigo da Su Najeriya

An Shiga Fargaba da Aka Kama Tulin Makamai Ana Yunƙurin Shigo da Su Najeriya

  • Jami'an hukumar kwastam sun yi nasarar cafke wasu manyan makamai da aka shigo da su cikin ƙasar nan ta jihar Legas
  • Rahotanni sun nuna shugaban hukumar kwastam ta Najeriya (NCS), Adewale Adeniyi ya isa Legas domin zantawa da manema labarai
  • Wannan ba shi ne karo na farko da kwastam ke kama makamai ba a daidai lokacin da ake fama da matsalolin tsaro a sassa daban-daban

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Lagos - Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS) ta kama adadi mai yawa na bindigogi da alburusai da aka shigo da su ƙasar nan ba bisa ƙa'ida ba a jihar Legas.

Ko da yake ba a bayyana ƙimar waɗannan makamai ba tukuna, an tabbatar da cewa adadin su yana da yawan gaske.

Shugaban kwastam.
Jami'an kwastam sun kama makamai ana shirin shigo da su cikin ƙasa a Legas Hoto: NCS
Asali: Facebook

Kwanturola Janar na Kwastam, Adewale Adeniyi, ya isa Legas domin yi wa manema labarai bayani a Ofishin ayyuka na ƙasa (FOU) da ke Ikeja, in ji rahoton The Nation.

Kara karanta wannan

An kaddamar da shirin karban tuban 'yan bindiga da koya musu sana'o'i

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kwastam suna yawan kama makamai

Wannan nasara na zuwa ne a daidai ne lokacin da ake fama da matsalar tsato kama daga ƴan bindiga, ƴan fashin daji, da sauransu a sassan ƙasar nan.

Ba wannan ne karon farko da dakarun hukumar kwastam ke kama makamantan irin waɗannan makaman da ake shirin shigo da su Najeriya ba.

A cikin watan Yulin 2024, jami'an kwastam sun kama fiye da bindigogi 800 da alburusai 100,000 da aka ɓoye a cikin kwantena a tashar jiragen ruwa.

A shekaru da da dama da suka gabata, Hukumar Kwastam ta yi nasarar kama makamai da alburusai masu ɗumbin yawa daga hannun masu fasa kwaurinsu.

Yadda kwastam ke ba da gudummuwa

A cewar rahoton da aka fitar a watan Oktoba 2024, hukumar ta kama makamai 10,498 da alburusai 114,929 tun daga shekarar 2018, wanda darajar su ta kai Naira biliyan 9.58.

Kara karanta wannan

Katsina: Likitan da ke kula da lafiyar 'yan ta'adda ya shiga hannun jami'an tsaro

Bayanai sun nuna cewa kashi 60% na makaman da kwastam suka cafke ana shirin shigo da su Najeriya, an kama su ne a bara.

Waɗannan nasarori suna nuna ƙoƙarin da Hukumar Kwastam ke yi wajen hana shigo da makamai ba bisa ƙa'ida ba, wanda hakan na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da tsaro a ƙasar nan.

Nasarorin jami'an kwastam a shekarar 2024

A wani labarin, kun ji cewa hukumar kwastan ta Najeriya (NCS), ta bayyana cewa jami'anta sun kama motoci 397 da darajarsu ta kai Naira biliyan 5.64 a 2024.

Hukumar ta ƙara da cewa bayan wannan, ta kuma kama magunguna 175,676 da kwantena 6,271 na jabun magunguna da darajarsu ta kai Naira biliyan 3.04.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel