Badaru Ya Fadi Dalilin Tinubu Na Bashi Ministan Tsaro a Gwamnatinsa

Badaru Ya Fadi Dalilin Tinubu Na Bashi Ministan Tsaro a Gwamnatinsa

  • Ministan tsaron Najeriya, Mohammed Badaru, ga taɓo batun muƙamin da ya samu a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu
  • Mohammed Badaru ya bayyana cewa rawar da ya taka a lokacin da yake mulkin jihar Jigawa, ta taimaka masa wajen samun muƙamin minista
  • Ministan ya bayyana cewa hanyoyin da ya bi wajen samar da tsaro a Jigawa na taimaka masa a yanzu da yake kan ministan tsaron Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ministan tsaro, Mohammed Badaru, ya yi magana kan samun muƙamin da ya yi a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Mohammed Badaru ya bayyana cewa an ba shi muƙamin ministan tsaro ne saboda ƙwarewarsa a wajen gudanar da mulki.

Badaru ya magantu kan zama minista
Badaru ya ce ya samu gogewa a harkokin mulki Hoto: Mohammed Badaru Abubakar
Asali: Facebook

Ministan ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Naɗin da aka yi wa Badaru a matsayin ministan tsaro, ya sa an kauce daga al'adar naɗa mutanen da ke da alaƙa da harkar tsaro a muƙamin.

Kara karanta wannan

Hafsan hafsoshi ya gano bakin zaren kan samar da tsaro a Najeriya

Badaru ya magantu kan zama ministan tsaro

Sai dai, Badaru ya bayyana cewa rawar da ya taka a lokacin da yake gwamnan Jigawa, ta taimaka wajen samun muƙamin ministan da ya yi.

"Naɗin da Shugaba Tinubu ya yi min na ministan tsaron Najeriya, ya nuna kaucewa daga al'adar naɗa mutanen da ke da tarihin aikin soja."
"An yi shi ne bisa gogewar da na samu a fannin gudanar da mulki, da kuma nasarorin da aka samu a fannin magance rikice-rikice, musamman a matsayina na tsohon gwamnan jihar Jigawa."
"Hanyar da na bi wajen samar da tsaro a Jigawa ya haifar da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki. Ƙwarewar da na samu ta yi tasiri a matsayina na ministan tsaro."

- Mohammed Badaru

Badaru ya yi ta'aziyyar rasuwar Lagbaja

A wani labarin kuma, kun ji cewa ministan tsaron Najeriya, Mohammed Badaru Abubakar ya yi magana kan rasuwar Laftanar-janar Taoreed Lagbaja.

Kara karanta wannan

"Najeriya na bukatar mace ta zama shugaban ƙasa," Babban sarki ya yi bayani

Mohammed Badaru ya jajantawa shugaban ƙasa Bola Tinubu kan rasuwar hafsan sojoji da aka yi a Najeriya inda ya ce mutuwsrsa babban rashi ne.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

iiq_pixel