Tinubu zai Gabatar da Bukatu 2 a Taron Kasashen Musulunci da Larabawa a Saudiyya
- Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu zai mika wasu manyan bukatu a taron kasashen Larabawa da Musulmi a Saudiyya
- Daga cikin bukatun da ake sa ran Bola Tinubu zai gabatar akwai dakatar da yakin da Isra'ila ke kai wa kan Falasdinawa
- Tinubu ya sauka a birnin Riyadh da ke Saudiyya domin halartar babban taron da za a gudanar da tsawon kwanaki biyu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Saudi Arabia – Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sauka a birnin Riyadh da ke Saudiyya domin halartar taron Larabawa da kasashen Musulunci inda zai mika bukatu kan yakin Isra'ila.
An gano wasu daga cikin bukatun da shugaba Tinubu zai gabatar a gaban taron bayan an fara za su danganci yakin da aka shafe sama da shekara ana yi tsakanin Isra'ila da Falasdinawa.

Source: Facebook
Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa Yarima Mohammed AbdulRahman ne ya tarbi Bola Ahmed Tinubu a ranar Lahadi a filin jirgin Sarki AbdulAziz.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Bukatun da Tinubu zai gabatar a Saudiyya
Voice of Nigeria ta tattaro cewa shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu zai bukaci tsagaita wuta a yakin da Isra’ila ke kai wa kan Falasdinawa.
Haka kuma ana sa ran shugaban zai nemi a samar da tsarin kasa biyu a Falasdinu yayin da Isra'ila ke kokarin fitar da mazauna Gaza da wasu sassan daga muhallansu.
Abin da za a tattauna a kasar Saudiyya
Taron kasashen Larabawa da na musulunci da ke gudana a Saudiyya ya na mayar da hankali a kan yakin da Isra’ila ta kaddamar a kan Falasdinawa.
Dakarun Isra’ila na IDF sun kashe Falasdinawa akalla 43,391 tun bayan fara yakin a shekarar 2023 zuwa yanzu, daga cikinsu akwai kananan yara da mata.
Shugaba Tinubu ya sauka a Saudiyya
A baya mun ruwaito cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya sauka a filin jirgin Yarima Mohammed AbdulRahman da ke Saudiyya domin halartar kasashen Larabawa da na Musulunci.
Za a gudanar da taron na kwanaki biyu inda ake hasashen za a tattauna manyan batutuwa da su ka hada da kasuwanci, yaki da ta'addanci da ci gaban ababen more rayuwa tsakanin kasashen.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng

