Sai bayan Mako 2: An Kara Shiga Ruɗani kan Gyaran Wutar Arewa
- Gwamnatin tarayya ta kara bayani kan lokacin da wutar lantarki za ta kammala dawowa a jihohin Arewacin Najeriya
- Ministan makamashi, Adebayo Adelabu ya tabbatar da sai ranar 12 ga watan Nuwamba za a kammala gyaran wutar Arewa
- Hakan na zuwa ne bayan an shafe kwanaki 10 babu lantarki a jihohi 17 a yankin Arewacin Najeriya saboda lalacewar layin wuta
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
FCT, Abuja - Ministan makamashi, Adebayo Adelabu ya yi bayani kan samun cikakken gyaran wutar lantarki a Arewacin Najeriya.
Adebayo Adelabu ya ce shawo kan matsalar dari bisa dari zai dauki kimanin mako biyu masu zuwa.

Source: Twitter
Jaridar Punch ta wallafa cewa Adebayo Adelabu ya yi bayani ne ga Sanatocin Najeriya a kan matsalar lantarkin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Za a yi mako 2 kafin gyara wutar Arewa
Ministan makamashi, ya tabbatar da cewa kafin a kammala gyaran wutar lantarki a Arewacin Najeriya dari bisa dari, za a dauki mako biyu, zuwa 12 ga Nuwamba.
Adebayo Adelabu ya bayyana haka ne a gaban majalisar dattawan Najeriya yayin da yake bayani kan halin da ake ciki.
"Ina mai tabbatar muku cewa nan da kwanaki 14 za a kammala gyaran wutar kuma za a samu cikakkiyar wutar lantarki.
Muna aiki da jami'an tsaro domin samun isa wajen gyaran wanda a yanzu haka yan bindiga ke kewaye da shi."
-Adebayo Adelabu, ministan makamashi
Maganar gyaran wuta ta wucin gadi
Sai dai ministan ya kara da cewa za a yi gyaran wucin gadi a tsawon kwanaki uku zuwa biyar domin fara samun wutar.
Business Day ta wallafa cewa a yanzu haka jihohin Kwara da Neja ne kawai ke samun wutar lantarki a yankin Arewacin Najeriya.
Hakan na nuni da cewa dukkan sauran jihohi 17 na Arewacin Najeriya na fama da matsalar wutar lantarki.
Gwamnati za ta kafa wutar sola a Arewa
A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin tarayya ta fara shirin samar da wuta mai amfani da hasken rana a jihohin Arewa.
Ministan makamashi, Adebayo Adelabu ya tabbatar da cewa an fara magana da yan kwangila kan yadda za a kafa wutar sola a Arewa.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng

